Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya fada jiya Litinin cewa, dole ne Isra’ila ta kara kaimi wajen bada damar kai agajin jinkai a zirin Gaza da aka yi wa kawanya.
Tawagar Hamas za ta ziyarci birnin Alkahira a yau Litinin da nufin ganin an cimma matsayar tsagaita bude wuta, kamar yadda wani jami'in Hamas ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters a ranar Lahadi.
Matakin da Hukumar ta CSC ta dauka ya hada da bada umarnin dakatar da sake yada rahoton nan take tare da dakatar da shirye-shirye kafafen yada labaran kasa da kasar 2 tsawon makonni 2.
Wasu jami'an Amurka biyu sun shaida wa kamfanin dillacin labarai na Reuters a ranar Talata cewa Amurka na shirin bayar da tallafin soji na dala biliyan 1 ga Ukraine, wanda shi ne na farko da za a samu daga kudirin dokar Ukraine da Isra'ila da ba a sanya wa hannu ba tukunna.
A yau Laraba ne Amurka da Rasha za su yi jayayya kan batun kai makamin Nukiliya a sararin samaniya a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, wanda zai kada kuri’a kan wani kudiri da Amurka ta gabatar wanda ke kira ga kasashen da su hana gasar kai makamai a sararin samaniya.
Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira a ranar Talata cewa a yi "bincike dalla dalla, na gaskiya kuma tabbatacce" na wasu manyan kaburbura da aka gano a wasu manyan asibitoci biyu a Gaza da ke fama da yaki da sojojin Isra'ila suka kai wa hari.
Hare-haren da Isra'ila ta kai a kudancin Gaza cikin dare ya yi sanadiyar mutuwar mutum 22 ciki har da yara kanana 18, jami'an kiwon lafiya suka ce a fada a ranar Lahadi, a daidai lokacin da Amurka ke kokarin neman amincewa da karin biliyoyin daloli na taimakon sojojin Isra'ila, kawarta.
Wani zakaran dara na wasan Chess, ‘dan Najeriya kuma mai fafutukar koyar da ilimin yara yana kokarin buga dara na tsawon sa'o'i 58 ba tare da tsayawa ba a dandalin Times Square na birnin New York domin karya tarihin duniya na tsawon wasan chess mafi dadewa.
Kamfanin Dillancin Labaran Iran na IRNA, ya ce tuni hukumomin kasar suka dana makaman dakile hare-hare a sararin samaniyar lardunan kasar da dama.
Ambaliyar ruwa ta rufe manyan titunan birnin Dubai kuma babban filin jirgin samansa ya kasance cikin rudu yayin da cibiyar hada-hadar kudi ta Gabas ta Tsakiya din ta kasance a kulle a ranar Laraba, kwana guda bayan da aka yi ruwan sama mai tsananin gaske da ba a taba irinsa ba.
'Yan sandan kasar Brazil da ke bincike kan gano wani karamin jirgin ruwa cike da gawarwaki sun ce akwai yiwuwar gawarwakin na 'yan ci-rani ne daga kasashen Mali da Mauritania a nahiyar Afrika.
Shugabannin duniya sun bukaci Isra'ila da kada ta mayar da martani bayan da Iran ta kai harin da ya hada da daruruwan jirage marasa matuka, da makamai masu linzami da kuma sauran makamai.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.