Firaiminista Benjamin Netanyahu ya fada a ranar Alhamis cewa barazanar da Amurka ta yi na hana makamai ba za ta hana Isra’ila ci gaba da kai hare-hare Gaza ba, lamarin da ke nuni da cewa za ta iya yin gaban kanta wajen mamaye birnin Rafah mai cunkoson jama’a ba tare da goyon bayan babbar kawarta ba
Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce da sanyin safiyar Juma’a Yarima Harry zai gana da Babban Hafsan Hafsoshin rundunar tsaron Najeriya, Janaral Christopher Gwabin Musa.
Shugaba Joe Biden ya fada jiya Laraba cewa ba zai aika da muggan makamai ga Isra'ila da za ta iya amfani da su wajen kai hare-haren wuce gona da iri kan Rafah ba, wanda yake tungar karshe ta Hamas a Gaza, saboda nuna damuwa kan yadda zai afka kan fararen hula fiye da miliyan 1 da ke fakewa a wurin.
Duk da cijewar da tattaunawar Isira'ila da Hamas ta yi, Amurka na fatan bangarorin biyu za su cimma jituwa kan sauran bambancin da ke tsakaninsu don a samu tsagaita wuta.
Putin ya sake samun sabon wa’adin mulki na shekaru 6 a watan Maris din daya gabata bayan daya lashe zaben shugaban kasar da aka yi ba tare da wata hamayya ba.
Kungiyar mayaka ta Falasdinu a jiya Litinin ta amince da shawarar tsagaita bude wuta a Gaza daga masu shiga tsakani, sai dai Isra'ila ta ce sharuddan ba su biya bukatunta ba, kuma za ta ci gaba da kai hare-hare a Rafah yayin da take shirin ci gaba da tattaunawa kan yarjejeniyar.
Isra'ila ta ba da umarnin rufe ofisoshin gidan talabijin na Aljazeera na Qatar da ke kasar a ranar Lahadin da ta gabata, lamarin da ya kara dagula takaddamar da ke tsakanin tashar watsa labaran da gwamnatin Firaminista Benjamin Netanyahu.
Wani jami'in Amurka ya fada a ranar Alhamis cewa Rasha ta tura wasu sojojinta zuwa wani sansanin sojin sama a Jamhuriyar Nijar inda wasu 'yan tsirarun sojojin Amurka suka rage bayan da akasarin sojojin Amurka suka fice daga sansanin da ke Yamai babban birnin kasar.
Daruruwan ‘yan sanda masu hular kwano ne suka kutsa da karfin tuwo zuwa tsakiyar wani filin taro a Jami’ar California a birnin Los Angeles da safiyar yau Alhamis domin wargaza sansanin da masu zanga zangar goyon bayan Falasdinawa suka kafa da magoya bayan Isra’ila suka kai musu hari cikin dare.
Nan bada dadewa ba tawagar Kungiyar Hamas ta Falasdinawa zata isa kasar Misra domin shiga tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza, a cewar wata sanarwar da kungiyar ta fitar yau Alhamis.
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya bayyana a ranar Laraba cewa, Turkiyya za ta bi sahun Afirka ta Kudu wajen shigar da kara kan kisan kiyashin da Isra'ila ke yi a kotun kasa da kasa (ICJ).
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya fada jiya Litinin cewa, dole ne Isra’ila ta kara kaimi wajen bada damar kai agajin jinkai a zirin Gaza da aka yi wa kawanya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.