Sanarwar da ‘yar mutumin, Nadine Jawad ta fitar ta bayyana cewa harin Isra’ila ta sama a kasar Lebanon ne ya kashe mahaifinta a Talatar da ta gabata “yayin da yake kokarin ceton wasu mutane.”
Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Fara Shirin Kwaso mutanen da ke zama a kasar Lebanon, biyo bayan ta'azzarar rikici tsakanin Isra'ila da Iran.
Cikin daren Laraba, dakarun Isra’ilan sun kai wasu sabbin hare-haren sama a wata tungar mayakan Hezbollah da ke wajen kudancin birnin Beirut.
A yau Laraba, rundunar sojin Isra’ila ta bayyana cewar dakarun sojin kasanta dana motocin sulke zasu shiga cikin samamen da take kaiwa yankin kudancin Lebanon domin zafafa hare-haren da take kaiwa kungiyar Hizbullahi
Hakan na zuwa ne ‘yan kwanaki kadan bayan Israi’la ta kashe shugaban kungiyar Hezbollah, Hassan Nasrallah, da kwamandojinsa.
Fafatawar Walz da Vance zai kasance a yau Talata 1 ga watan Oktoba da karfe 9 na dare agogon ET da Laraba 2 ga watan Oktoban da muke ciki da karfe 1 na safe agogon UTC.
A yau Talata, rundunar sojin Isra'ila ta gargadi al'ummomin dake zaune a yankunan kan iyakar Lebanon dasu kaurace daga kusan garuruwa 24 bayan da ta kaddamar da samamen da ta kira da kwarya-kwaryan kutse ta kasa akan mayakan kungiyar Hezbollah
Mummunar gobarar ta babbake motar dake kan wata babbar hanya a yankin arewacin birnin Bangkok yayin da take dauke da yara 38-da suka hada da kanana da matasa da malamai 6 dake balaguron 'yan makaranta.
Mutombo wanda aka haifa a Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo, da fari ya zo jami'ar Georgetown dake Washington ne a bisa tallafin karatu a shekarar 1987, sannan yayi shura sa'ilin daya shiga kungiyar wasan kwallon kwando yana shekararsa ta 2.
A yau Litinin, fadar Kremlin ta yi Allah-wadai da kisan Shugaban Hizbullahi Hassan Nasrallah da hare-haren Isra’ila ta sama su ka yi a makon da ya gabata sannan tace tana da hasashe mai karfi dake nuna yiyuwar fadadar yaki a yankin Gabas ta Tsakiya.
Shugaban Hezbollah na riko ya sha alwashin ci gaba da yakar Isra’ila sannan ya bayyana cewar a shirye kungiyar take ta shafe dogon zango tana yaki duk kuwa da cewar an hallaka manyan kwamandojinta, ciki harda jagoranta, Hassan Nasrallah.
Yayin da daruruwan iyalai ke kwanciya a kan titunan Beirut, hukumomin kasar ta Lebanon sun ce mutanen da suka rasa muhallansu sun kai miliyan daya.
Domin Kari
No media source currently available