Ya shaida wa manema labarai cewa, “Batun da ya fi muhimmanci a yau shine tsagaita wuta, musamman a Lebanon da kuma Gaza.”
Macron ya nanata damuwarsa kan rikicin Gaza da ke ci gaba, duk da kiran da ake ta yi na a tsagaita wuta.
Hezbollah tace mayakan ta na yin fito na fito da dakarun Isra’ila a yankin kudancin kan iyakar Lebanon, inda dakarun Isra’ila sukace sun kaiwa mayakan da Iran ke marawa baya hari a wani masallaci.
Firai Ministan Garry Conille ya fada a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa, “Za’a farauto wadanda suka aikata laifin tare da gurfanar da su a gaban kuliya, ba tare da bata lokaci ba.”
Hukumomin kasar sun rufe manyan tituna da hanyoyi shiga cikin birnin da kwantenonin jigilar kaya.
Rundunar ta IDF ta fada a ranar Alhamis cewa, wani harin da Isra’ila ta kai da jiragen yakinta ya kashe wani kwamandan Hezbollah Khader Al-Shahabiya.
Sanarwar da ‘yar mutumin, Nadine Jawad ta fitar ta bayyana cewa harin Isra’ila ta sama a kasar Lebanon ne ya kashe mahaifinta a Talatar da ta gabata “yayin da yake kokarin ceton wasu mutane.”
Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Fara Shirin Kwaso mutanen da ke zama a kasar Lebanon, biyo bayan ta'azzarar rikici tsakanin Isra'ila da Iran.
Cikin daren Laraba, dakarun Isra’ilan sun kai wasu sabbin hare-haren sama a wata tungar mayakan Hezbollah da ke wajen kudancin birnin Beirut.
A yau Laraba, rundunar sojin Isra’ila ta bayyana cewar dakarun sojin kasanta dana motocin sulke zasu shiga cikin samamen da take kaiwa yankin kudancin Lebanon domin zafafa hare-haren da take kaiwa kungiyar Hizbullahi
Hakan na zuwa ne ‘yan kwanaki kadan bayan Israi’la ta kashe shugaban kungiyar Hezbollah, Hassan Nasrallah, da kwamandojinsa.
Fafatawar Walz da Vance zai kasance a yau Talata 1 ga watan Oktoba da karfe 9 na dare agogon ET da Laraba 2 ga watan Oktoban da muke ciki da karfe 1 na safe agogon UTC.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.