Wata Sanarwa dauke da sa hannun hadimin gwamnan jihar Sokoto akan harkokin yada labarai, Abubakar Bawa, ya musanta zargin ya kuma ce hakan na neman kawo cikas ga alakar da ke tsakanin gwamnatin jihar da fadar Sarkin Musulmi.
Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe Mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Danfodio da ke Sakkwato, Farfesa Yusuf Saidu.
Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a yau Alhamis yayin taron kolin zaman lafiya da tsaro a shiyar arewa maso yammacin Najeriya daya gudana a jihar Katsina.
Gwamnatin jihar Ogun a Najeriya ta tabbatar da kamuwar mutane 25 da cutar kwalara a kananan hukumomi bakwai na jihar, yayin da mutum daya ya rasa ransa a karamar hukumar Ijebu ta Arewar jihar.
Mataimakin shugaban kasar ya bayyana hakan ne a taron kolin zaman lafiya da tsaro a jihohin arewa maso yammacin Najeriya dake gudana a jihar Katsina da ake yadawa kai tsaye a tashar talabijin ta Channels.
Babban daraktan kungiyar MURIC, Farfesa Ishaq Akintola, ne ya bayyana damuwar a cikin sanarwar daya fitar a yau Litinin, inda yace al'ummar Musulmin Najeriya ba zasu amince da duk wani tunani na tube Sarkin Musulmi ba.
Hukumar hana sha da fataucin kwayoyi a Najeriya tace zata rika binciken wuraren da ake wannan dabi'ar da suka hada da gidaje da otel-otel, kuma duk wurin da aka kama da laifi za'a kwace shi a mallakawa gwamnatin tarayya.
Akalla mutane bakwai ne aka kashe tare da yin garkuwa da 100 a daren Asabar bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari a kauyukan jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya.
Manoma a Najeriya na kokawa akan tashin farashin takin noma inda suke kira ga gwamnatin kasar da ta duba lamarin su, yayin da wasu masana ke cewa dole ne a dauki matakan gaggawa, yayin da damina ke kara shigowa gadan-gadan.
Jami'an tsaro a Najeriya sun sanar da samun nasarar kashe wani kasurgumin dan bindiga mai suna Alhaji Kachalla Ragas, wanda ya shahara wajen kai hare hare da kuma satar mutane domin neman kudin fansa a wasu sassan jihar Kaduna da jihohi makwabta.
Yau shekaru 30 da suka gabata, kwallayen da rashidi yekini da daniel amokachi da emmanuel amunike suka ci sun taimakawa tawagar super eagles yin bajinta a fitowarta ta farko.
Sanarwar da ofishin hukumar mai kula da yankin gabashin Tekun Maditereniyan ya fitar tace, an samu barkewar annobar ne daga ranakun 1 ga watan Janairu zuwa 26 ga watan Mayun daya gabata.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.