Trump ya ayyana Gaza da “wurin da aka rusa” sannan ya kwatanta batun da sama wa mazauna zirrin Gaza da wani matsuguni a madadin inda suke da yaki ya daidaita.
Duk da jinkirta matakin a wasu fannoni, har yanzu akwai fargaba akan abin da zai kasance nan gaba a bangaren tallafin da Amurka ke bayarwa a fannin lafiya a fadin duniya.
'Muna kokarin ganin cewa mun yi sulhu don kawo karshen yake yaken da ake yi, ko kuma a kalla a ce mun taimaka don ganin sun yi sulhu tsakaninsu. Amma babu taimakon da ake bamu. Wannan shine babbar manufar MDD.'
Marigayi tsohon shugaban Amurka Jimmy Carter, manomin gaydar da ya lashe zaben shugaban kasar Amurka bayan rikicin Watergate da yakin Vietnam ya mutu a watan Disamban 2024 yana da shekaru 100 a duniya.
Saukin farashin da aka samu, ya dace da faduwar farashin man fetur a kasuwar duniya, sannan, kamfanin na Dangote, yana so talakwan Najeriya suma su ci moriyar saukin farashin da aka samu, domin su samu saukin tsadar rayuwar da ake fama da ita.
Yiwuwar janye tallafin Amurka a duniya na janyo muhawara a ciki da wajen kasar
Yayin da duniya ke ci gaba da fama da rikice rikice, wasu masu ruwa da tsaki na fatan manufofin Amurka karkashin Trump, na rage daukar matakan soji, zai taimaka wajen kawo kwanciyar hankali
"Daga karshe za su yi nadama duk kasashen 3 ba su da iyaka da teku in za su shigo da kaya sai ta Benin, Senegal ko Najeriya.”
Umarnin Zartarwar shugaba Trump zai dakatar da bada tallafin abinci ga yaran da suke fama da matsalar rashin abinci a Habasha
Wani dan jarida da ke Goma, ya fada wa Muryar Amurka ta wayar tarho cewa ana ci gaba da artabu a yankin tashar jirgin sama da ke birnin sannan ya ce da alamu fadan na dada ta’azara.
Sabon Sakataren Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka zai tabbatar da tasirin Amurka don ta maye gurbin China ta hanyar tabbatar da zaman lafiya a kudu maso gabashi da gabashin Asiya.
Shugaban Amurka Donald Trump ya yi shelar labta wasu nau’ukan haraji, da tsauraran matakan VISA, da kuma sauran wasu matakai na ramuwar gayya kan kasar Colombia, bayan da ta ki yadda wasu jiragen sojin Amurka biyu, dauke da bakin haure, su sauka a kasar.
Sojojin Isira’ila sun bude wuta kan Falasdinawa a yankunan Lebanon da Gaza har su ka kashe mutane 23 baya ga wadanda su ka raunata.
Mayakan Boko Haram da na ISIS Shiyyar Afurka Ta Yamma (ISWAP), da suka fi gudanar da harkokinsu a jahar Borno, sun auna jam’an tsaro da farar hula, wanda ta haka su ka hallaka 20 tare da kawar da dubban mutane.
IBB yayi hiraraki da kafafen yada labaran cikin gida da na kasashen waje tun bayan saukar shi daga kujerar mulkin Najeriya, yayi kokarin kaucewa batutuwa masu sarkakiya da suka faru a lokacin da yake Mulki.
Domin Kari