Mafusatan magoya bayan Shugaba Donald Trump sun fantsama cikin ginin Majalisar Dokokin Amurka a ranar Laraba a lokacin wata zanga-zanga. Turump ya yi kira ga zaman lafiya bayan an kammala rikicin amma bai bukaci magoya bayansa su watse ba. Tun daga farko ya ba su izinin zuwa titin Capitol Hill.
Har zuwa yau Laraba ba a tabbatar da jam’iyyar da za ta kasance mai rinjaye ba a majalisar dattawan Amurka a zabuka zagaye na biyu guda biyu da aka yi a jihar Georgia da ke kudancin kasar.
Da alamar su ma miyagun da ke gasa ma 'yan Najeriya aya a hannu sun kusa dandadawa, ganin yadda ake cigaba da kera ma Najeriya wasu jiragen yaki a Amurka, baya ga wasu matakan kuma da ake nazarin daukarsu.
A wata tattaunawa ta waya ta ba sabon ba, a ranar Asabar da ta gabata, Shugaban Amurka Donald Trump, ya roki jami'an zabe a jihar Georgia su samo mashi adadin kuri’un da za su bashi damar sauya sakamakon zaben kasar da aka yi wanda ya sha kayi Shugaba Joe Biden mai jiran gado kuma ya lashe.
Ana samun karin ‘yan majalisa daga jam’iyyar Republican da ke goyon bayan kokarin shugaba Donald Trump na sauya sakamakon zaben kasar da aka yi.
Shugaban da ya ki ya sanya hannu a kudurin tallafin, ya na mai cewa ya so a ba Amurkawa dala 2,000.
Wata motar tafi-da-gidanka ta tarwatsa kanta a cibiyar kasuwanci ta Nashville a jihar Tennessee ta Amurka a ranar bukin Krismeti, inda mutum uku suka jikata, lamarin da ‘yan sanda suka kwatanta da aikin kasar waje.
Jiya Talata zababben shugaban Amurka Joe Biden ya nuna juyayi ga iyalai masu gwagwarmaya, kuma ya yaba wa Majalisa don zartar da kudirin tallafin coronavirus yayin da kasar ke ci gaba da samun karuwar COVID-19 da ta addabi kowa ana shirin bikin Kirsimeti.
Matakan bada tallafin sun hada da taimaka wa masana'antu don ma'aikatansu su ci gaba da aiki, da kuma ba Amurkawa tallafin kudi na kai tsaye.
Sama da mutane miliyan 75 suka kamu da cutar COVID-19 a fadin duniya a cewar cibiyar da ke bin diddigin annobar coronavirus ta Jami’ar Johns Hopkins ranar Asabar 19 ga watan Disamba.
An yiwa ‘yan majalisar dokokin Amurka bayani a kan gagarumin kutsen yanar gizo da aka kai a kan cibiyoyin gwamnatin Amurka, kana sashen masu zaman kansu na kira ga kasar ta tashi tsaye, kashedi da aka yi da bayanai da aka tattara na nuni da Rasha ce take wannan aiki.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.