Shugabar majalisar wakilan Amurka Nancy Pelosi ta ce yau Litinin 'yan majalisar wakilai zasu gabatar da kudurin neman majalisar ministocin Trump ta yi amfani da dokar nan ta 25th Amendment, da ta bada dama a sauke shugaba daga mukaminsa.
'Yan jam’iyyar Democrat a Majalisar Dokokin Amurka, a jiya Lahadi, sun dau azamar tsige shugaban kasar Donald Trump, a dai-dai lokacin da wa’adin mulkinsa ke kawowa karshe.
Yayin da aka kara kama wasu daga cikin masu tarzomar da suka afka ginin majalisar dokokin Amurka ranar Larabar da ta gabata, Derrick Evans, dan majalisar wakilai a jihar West Virginia ya yi murabus daga mukaminsa saboda shiga wurin da sai da izini a majalasar.
A jiya Asabar sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo ya ce zai dage takunkumin mu’amala tsakanin jami’an Amurka da takwarorin su na kasar Taiwan, wani matakin da zai fusatar da China kana ya kara tankiya tsakanin Beijing da Washington a kwanakin karshe na mulkin shugaban Donald Trump.
Kashi 57 cikin 100 na Amurkawa na so a sauke shugaba Donald Trump daga mukaminsa ba tare da bata lokaci ba, bayan da shugaban ya karfafa zanga-zangar da aka yi a wannan makon wadda ta rikide ta koma mummunar tarzoma a cikin ginin majalisar dokokin Amurka.
Yayin da ake kara bayyana damuwa kan abin da ake tunanin shugaban Amurka Donald Trump ka iya aikatawa a cikin ‘yan kwanaki da suka rage masa ya sauka daga mulki, Pelosi ta fara neman hanyar hana shugaban daukar matakan soja.
Ranar Asabar 9 ga watan Janairu cibiyar samar da bayanan cutar coronavirus ta Jami’ar Johns Hopkins ta bada rahoton cewa mutane kusan miliyan 90 suka kamu da cutar ta coronavirus a fadin duniya.
Majalisar Dokokin Amurka ta tabbatar da nasarar Joe Biden na jam’iyyar Democrat a zaben shugaban kasa na watan Nuwamba shekarar da ta gabata.
A ci gaba da rangadin da ta ke yi a cibiyoyin tsaron Najeriya, sakatariyar harkokin sojin saman Amurka, Barbara Berrett ta jagoranci wata tawagar jami'ai biyar da suka gana da ministan tsaron Najeriya a birnin Abuja.
Jami’an tsaro na musamman sun isa ginin Majalisar Dokoki yayin da dokar hana fita ta fara aiki a babban birnin Amurka, sa’o’i bayan da magoya bayan Trump suka mamaye majalisar.
Magoya bayan Shugaba Donald Trump sun mamaye ginin Majalisar Dokokin Amurka na tsawon sa’o’i a ranar Laraba, 6 ga watan Janairu, kafin daga bisani jami’ai su ayyana cewa al’amura sun daidaita.
A dai dai lokacin da mataimakin shugaban Amurka Mike Pence, ke jagorantar 'yan Majalisun Amurka biyu a bikin tabbatar da kuri'un kwaleji da zababben shugaban kasa Joe Biden ya samu a zaben Nuwamba, magoya bayan Trump cikin fushi sun afkawa Majalisar tare da dakatar da wannan biki.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.