Firai ministan Birtaniya Boris Johnson ya fadawa shugaba Joe Biden cewa, a shirye yake ya bude sabon babi a yarjejeniyar kasuwancin Amurka da Birtaniya.
Rahotannin sun nuna cewa cutar coronavirus ce ta yi sanadiyar mutuwar Larry King, wanda shirinsa na "Larry King Live" na gidan talabijin din CNN ya tattaro miliyoyin 'yan kallo daga fadin duniya.
Ana kara matsawa gwamnatin Somalia lamba, yayin da ake zargi ta aika da sojojin Somalia din zuwa makwabciyar kasar Habasha domin su shiga mummunar yakin Tigray.
A ranar Litinin ne kakakin majalisar wakilai Nanacy Pelosi zata aike da bayani a kan tsige Donald Trump zuwa majalisar dattawa inji shugaban ‘yan Democrat a majalisar dattawan Chuck Schummer a jiya Juma’a.
Shugaban Amurka Joe Biden ya sanya hannu a kan wasu dokokin umarnin shugaban kasa hade, da zummar samar da tallafin kudi da na abinci ga iyalai da annobar coronavirus ta yi mummunar tasiri a kan su kana zasu taimakawa ma’aikatan tarayya.
Gwamnatin Biden ta soki matakin China na kakaba takunkumi kan wasu jami’an gwamnatin Trump a ranar Laraba, mintoci kadan bayan rantsar da Joe Biden a matsayin shugaban kasar Amurka na 46.
Shugaban Hukumar Kula da Kafafen Yada Labarai ta Amurka, USAGM ya sauka da yammacin jiya Laraba bisa bukatar gwamnatin Shugaba Joe Biden, jim kadan bayan da Biden ya hau mulki.
A karon farko cikin shekaru sama da goma jam'iyyar Democrat ta Amurka ta samu rinjaye a dukkan Majalisun Amurka.
Sabon shugaban Amurka ya soke dokokin dake hana ‘yan wasu kasashen musulmai da wasu kasashen Afirka shiga Amurka.
An rantsar da Dan Jam’iyyar Democrat Joe Biden, a yau Laraba a matsayin shugaban Amurka na 46 a Majalisar Amurka.
Ku kalli Shan Rantsuwar Joseph R. Biden da Kamala D. Harris da Za’a yi a Washington. Ranar Laraba 20 ga Watan Janairu Daga Karfe 11:30 na Safe Agogon Washington DC
Mai nazarin harkokin mulki a kasashen Afrika farfesa Boube Na Mewa na jami’ar Diof dake Dakar, Senegal ya bayyana cewa, a ganin sa zaben Trump babban kuskure ne.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.