An samu bullar sabon nau'in cutar COVID-19 na Birtaniya a Garin Los Angeles da ke jihar California a Amurka.
Yayin da tashin hankalin kungiyoyin bata gari, rashin ayyuka, da talauci suka addabe su, ayarin bakin na fatan isa Amurka don samun rayuwa mafi kyau.
Hukumomin tsaro kulle birnin Washington kana jami’an tsaron Amurka suna kara jan damarar tinkarar magoya bayan Trump da za su yi tattaki a manyan biranen jihohin Amurka 50 a karshen wannan mako.
A cikin sa’o’in farko da ya zama shugaban kasa, Joe Biden zai yi amfani da ikon shugaban kasa ya sauya wasu matakai masu tsarkakiya da Trump ya dauka a baya kana ya fara daukar matakan magance annobar coronavirus, inji shugaban ma’aikatan ofishin shugaban kasa mai jiran gado a jiya Asabar.
An rufe wasu tituna a kewayen ginin majalisar dokokin Amurka an kuma rufe wasu wuraren tarihi a birnin yayin da ake shirin rantsar da shugaba Joe Biden mai jiran gado ranar 20 ga watan Janairu.
A ci gaba da dauke hankalin duniya da abkawa Majalisar Dokokin Kasar Amurka da kuma tsige Shugaba Donald Trump karo na biyu da ya biyo baya, masana harkokin siyasar duniya na ci gaba da tsokaci game da tasirin wannan al'amarin.
Hukumomi a Amurka sun tsaurara matakan tsaro a birnin Washington DC yayin da ya rage kwanaki a rantsar da zababben Shugaba Joe Biden a matsayin shugaban Amurka na 46.
A karo na biyu cikin wa'adin mulkinsa na shekaru hudu Majalisar Wakilan Amurka ta sake tsige shugaban kasa Donald Trump. Kuma zai fuskanci shari'a a Majalisar Dattawa bayan sabon shugaban kasa ya fara aiki.
Sabanin yadda a baya aka yi ta muhawara, kan ko shugaban kasa zai iya yafe wa kansa laifi, yanzu abin ya zama muhimmiyar muhawara tun bayan da magoya bayan Trump su ka fusata tare da afkawa ginin Majalisar Dokokin Amurka.
A yau Laraba ake sa ran Majalisar Wakilan Amurka za ta kada kuri’a akan sake tsige shugaba Donald Trump karo na biyu, abin da ba a taba yi ba a tarihin Amurka.
A yau Laraba ne ake kyautata zaton Majlisar Wakilan Amurka mai rinjayin Democrat ke kada kuri’a a kan tsige Shugaba Donald Trump a karo na biyu, wani mataki da ya biyo bayan tarzoma da magoya bayansa suka yi a Majalisar Dokokin Kasa.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.