Mai tsaron gida na Uruguay Sergio Rochet ya buge feneratin da Eder Militoa na Brazil ya buga ta farko, yayin da abokin wasansa Douglas Luiz ya bugi raga ta fita, wanda hakan ya bai wa Uruguay nasara.
Jam'iyyar Labour ta Birtaniya ta karbe mulki a yau Juma'a bayan shafe sama da shekaru goma tana adawa, yayin da 'yan adawa suka bai wa jam'iyyar gagarumar nasara.
Hukumar da ke sa ido kan kafafen yada labarai na Radio da Talbijin ta Kasar Turkiyya RTUK ta kwace lasisin wata tashar Radio mai zaman kanta a ranar Laraba, sakamakon barin baki game da kisan kiyashin da aka yi a Armenia, a tashar.
A yau Alhamis ne 'yan Burtaniya suka kada kuri'ar zaben 'yan majalisar dokokin kasar.
Kungiyar Hezbollah ta kasar Labanon ta ce ta harba rokoki sama da 200 ne a wasu sansanonin soji da ke Isra'ila a matsayin ramuwar gayya kan harin da ya kashe daya daga cikin manyan kwamandojinta.
Matsanancin cunkoso da rashin mafita ne ya haifar da wani turmutsitsi a wani bikin addini a arewacin Indiya da ya hallaka mutane da dama, in ji hukumomi a ranar Laraba.
Karin tashe tashen hankulla ya kara Kamari ne a karshen watan Fabrairu, bayan dimbin jerin shiryayyun hare hare kan muhimman gine ginen gwamnati da sannu a hankali ya kai ga Priministan kasar Ariel Henry ya tattara shugabancin kasar ya ajiye a watan Apirilu.
Jam’iyun adawa na Faransa sun kulla wata yarjejeniya cikin sauri domin kokarin kange nasarar kud da kud ga yar jam’iya mai ra’ayin rikau, Marine Le Pen.
Guguwar Beryl ta ratsa kan ruwa a ranar Talata a matsayin wata mummunar guguwa mai rukuni 5 a kan hanyar da za ta bi kusa da Jamaica da tsibirin Cayman bayan da ta afkawa yankin kudu maso gabashin Caribbean, inda ta kashe akalla mutane biyu.
Wani hari da Isra'ila ta kai ya kashe akalla mutane tara a birnin Khan Younis da ke kudancin Gaza, a cewar jami'an kiwon lafiya na Falasdinu a ranar Talata.
Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdoğan ya bayyana cewa, Turkiyya na tsaye tsayin-daka da kasar Labanon a daidai lokacin da ake ci gaba da samun takun saka tsakaninta da Isra'ila, ya kuma yi kira ga kasashen yankin da su marawa Beirut baya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.