A yau Lahadi Shugaban Amurka Joe Biden ya sanar a cikin wata wasika da ya aikewa al'ummar kasar cewa ba zai sake tsayawa takara ba kuma ya dakatar da yakin neman shugabancin kasar da yake yi ta bana.
Kasar Pakistan ta yi Allah wadai da gazawar kasar Jamus na kare karamin ofishin jakadancinta a Frankfurt da aka bayar da rahoton cewa wasu masu zanga zanga dauke da tutar kasar Afghanistan suka kutsa kai tare da lalata ofishin a ranar Asabar.
Biyo bayan wani mummunan hari da mayakan Houthi su ka kai a birnin Tel Aviv a kwanan nan, Isra'ila ta kai wa 'yan tawayen hari a Yemen har mutane uku suka mutu.
Sannu a hankali layukan internet na kamfanonin jiragen sama sun fara dawowa yau Asabar bayan da kamfanonin sadarwa na duniya, da bankuna da cibiyoyin hada-hadar kudi suka fada cikin rudani sakamakon gagarumar katsewar layukan internet a cikin 'yan shekarun nan, don aikin sabunta matakin kariya.
An kashe akalla mutane 13 a wasu hare-hare uku da Isra’ila ta kai kan sansanonin ‘yan gudun hijira da ke tsakiyar Gaza cikin dare zuwa yau Asabar, a cewar jami’an kiwon lafiyar Falasdinu, yayin da ake ganin ana samun ci gaba a tattaunawar tsagaita bude wuta a birnin Alkahira.
Kazalika matsalar ta shafa har da wasu kafafen yada labarai wadanda suka kasa watsa shirye-shiryensu.
Wani jirgi mara matuki kirar Iran da 'yan tawayen Houthi na Yemen suka tura a birnin Tel Aviv ranar Juma'a, ya yi sanadin mutuwar mutum guda tare da raunata akalla 10 a harin farko da kungiyar ta kai kan Isra'ila.
A ranar Alhamis din nan Priministan Izra’ila Benjamin Netanyahu ya ziyarci dakarun Izra’ilan a kudancin Gaza, a yayin da tankokin yakin Izra’ilan ke kara nausawa cikin Rafah.
Sabuwar zakaran kofin kasashen nahiyar Turai ta Euro 2024 Sifaniya ta koma ta uku a jerin jadawalin hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA da aka fitar a ranar Alhamis, yayin da Argentina da ta lashe gasar cin kofin duniya ta ci gaba da zama a matsayi na daya bayan da ta lashe kofin Copa America.
A wani samamen kasa da kasa da ya maida hankali akan kungiyoyin batagarin dake aikata laifuffuka a nahiyoyi 5 masu tushe a kasashen yammacin Afrika, ‘yan sanda sun kama mutane 300 sun kwace tsabar kudi dala miliyan 3 da toshe asusun banki 720, a cewar rundunar ‘yan sandan kasa da kasa ta Interpol.
Hukumomin kasar Thailand sun bayyana a yau Laraba cewar, binciken farko da aka gudanar akan musabbabin mutuwar gawa ya nuna cewar akwai burbushin sinadarin cyanide a jinin wasu ‘yan vietnam 6 da baki Amurkawa a otel din “Central Bangkok Luxury”
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.