Tawagar kwallon kafar Sifaniya ta lashe kofin kasashen nahiyar Turai bayan da ta ci takwararta na kasar Ingila da ci 2-1
Dr. Faruk Bibi Faruk, na jami’ar Abujan Najeriya ya ce wannan al’amari bai rasa nasaba da al’adar barin kusan kowa ya mallaki bindiga da kuma yadda siyasar Amurka ta fara daukar zafi.
A cewar jami'an binciken FBI mai kula da shiyar Pittsburgh, Kevin Rojek, hukumar bata san dalilin kai harin daya hallaka mutum guda tare da raunata wasu mutane 2 ba.
Gidan rediyon ma’aikatar sojan Isra’ila ta fada yau Asabar cewa sojojin Isra'ila sun auna shugaban sojan Hamas a wani hari a Khan Younis a Gaza, harin da ma’aikatar lafiyar wurin ta ce ya kashe akalla Falasdinawa 20.
Kasashen kungiyar NATO sun caccaki China, Iran, Koriya ta Arewa A Kan mara wa Rasha baya a mamayar da ta ke yi wa Ukraine.
Shahararrun ‘yan kasuwa na duniya da ‘yan siyasa sun fara hallara babban birnin kasar India a ranar Juma’a domin halartar daurin auren karamin dan Mukesh Ambani, wanda ya fi kowa arziki a Asiya.
A ranar Alhamis ne Rasha sa sanya sunan Yulia Navalnaya, wata fitacciyar yar adawa a Rasha, kuma mai dakin marigayi Alexey Navalny, kan jadawalin ta na jerin sunayen 'yan taadda da masu tsatstsauran ra’ayi.
A yau Alhamis kasar China ta zargi kungiyar tsaro ta NATO da kokarin tabbatar da tsaro ta ko wane irin hali tare da shaidawa kawancen kasashen da kada ya haddasa makamancin wannan rudani a nahiyar Asiya.
Hukumomin asibiti sun bayyana cewar, hare-haren Isra’ila takai tsakiyar zirrin gaza ta sama da sanyin safiyar yau Laraba, sun hallaka Falasdinawa 20, ciki har da kananan yara 6 da mata 3, wasunsu ma na zaune ne a wurin da sojin Isra’ilar suka ayyana da tudun mun tsira.
A yau Talata, Babban Jami’in Majalisar Dinkin Duniya akan kare hakkin bil adama ya bayyana cewar ofishinsa na bibiyar rahotanni game da wani makeken kabari a rairayin Sahara dake kan iyakar kasashen Libya da Tunisiya bayan da a farkon shekarar nan aka gano gawarwakin bakin haure 65 a wani wuri daban
Rasha ta kai hari da makami mai linzami kan wani asibitin yara da ke babban birnin Ukraine a jiya Litinin, daya daga cikin hare-haren da ta ke kaiwa a yankunan kasar da ya wuce gona da iri, harin dai ya yi sanadiyar mutuwar mutane 31 tare da jikkata wasu 154.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron a ranar Litinin ya bukaci firaministansa da ya ci gaba da kasancewa a kan mukamin a halin yanzu.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.