Shugaban Amurka Joe Biden ya fada cikin wata sanarwa cewa, al’ummar Haiti sun cancanci zama lafiya a gidajen su, su gina ingantacciyar rayuwa ga iyalan su, su kuma more yancin demokradiyya
Mutumin da ya kafa WikiLeaks Julian Assange zai amsa laifin da ake tuhumarsa da aikatawa a wata yarjejeniya da ma’aikatar shari’a ta Amurka, da za ta sa ya kauce tafiya gidan yari, da kuma kawo karshen yiwuwar wata doguwar shari'a da ta ta’allaka kan buga wasu tarin takardu na sirri.
Yankin Dagestan da ke kudancin kasar Rasha ya gudanar da zaman makoki na kwanaki uku a yau Litinin bayan wani harin da mayakan Islama suka kai inda suka kashe mutane 19.
Wasu fashe-fashe sun yi sanadin tashin gobara a wata masana'anta ta batirin lithium a Koriya ta Kudu a ranar Litinin, inda suka kashe ma'aikata 22, mafi yawansu 'yan kasar China, yayin da kamfanin ya kone kurmus.
Wadansu ma’aurata daga Bowie, jihar Maryland na daga cikin sama da mutane dubu daya da suka rasu sakamakon matsanancin zafi yayin aikin hajjin bana a kasar Saudiya.
Firai Ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya fadi cewa dakarun kasarsa sun kusa kawo karshen "lokacin zafafa kai hare hare kan mayakan Hamas a Gaza na ba da jimawa ba.
Kasar Argentina mai rike da kofin ta lallasa Canada da ci 2-0 a wasan farko na gasar cin kofin Copa America da aka buga a Atlanta na jihar Georgia da ke Amurka a ranar Alhamis.
Ofishin jakadancin Amurka da ke Gaborone ya fitar da wata sanarwa inda ya ce Amurka za ta dauki nauyin shirya wani taro da zai tattaro manyan jami'an tsaro na kasashen Afirka a Botswana A mako mai zuwa
Jami'an Amurka sun ce suna aiki ta hanyar diflomasiyya don ganin an kawar da barkewar mummunan fada tsakanin Isra'ila da mayakan Hezbollah masu samun goyon bayan Iran da ke kudancin Lebanon.
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya rattaba hannu kan wasu jerin yarjeniyoyi da takwaransa na kasar Vietnam To Lam a yau Alhamis, yayin wata ziyarar aiki da ya kai kasar a daidai lokacin da Moscow ke neman karfafa alaka a nahiyar Asiya.
Guguwar da aka yi mata lakabin Alberto ta yi kaca-kaca da arewa maso gabashin Mexico da sanyin safiyar Alhamis a matsayin guguwar farko da aka ambata a kakar bana, dauke da ruwan sama mai karfi da ya yi sanadin mutuwar mutane uku, amma ya kawo jimami mai kyau ga yankin mai fama da matsanancin fari
Akalla mutane biyu ne suka mutu yayin da wasu tara suka jikkata yau Alhamis a lokacin da wani jirgin kasa dauke da fasinjoji ya yi ci karo da wani jirgin kasa mai gwajin aiki a babban birnin kasar Chile, Santiago.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.