Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan a ranar Laraba ya kai ziyararsa ta farko a Masar tun shekara ta 2012, inda ya gana da Shugaba Abdel Fattah al-Sisi
Tarayyar Turai EU, ta kudiri aniyar sake daura damara da ganin an sake tsugunar da tubabbun mayakan Boko Haram a kasashen yankin tafkin Chadi domin aiwatar da cikakken zaman lafiya.
An sako wata Likita ‘yar kasar Poland da aka yi garkuwa da ita a Chadi kuma tana cikin "koshashiyar lafiya," in ji ministan harkokin wajen Poland a ranar Talata.
"Isra'ila ta yi imanin cewa tana da ikon yin yadda ta ga dama," in ji ministan harkokin wajen kasar Naledi Pandor.
Isra'ila da Hamas na ci gaba da tattaunawa kan samun yarjejeniyar da ke da nufin samun tsagaita wuta da kuma 'yantar da mutanen da aka yi garkuwa da su a zirin Gaza, a cewar jami'ai biyu da ke da masaniya kai tsaye kan tattaunawar.
Shugaban Amurka Joe Biden ya shiga TikTok a ranar Lahadin da ta gabata, inda a karon farko ya wallafa wani bidiyo na dakika 26 a kafar sada zumuntar ta Tiktok.
'Yan sanda a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango sun harba barkonon tsohuwa a ranar Litinin don tarwatsa masu zanga-zangar da suka kona tayoyi da tutocin Amurka da na Belgium a kusa da ofisoshin jakadancin kasashen Yamma da na MDD a birnin Kinshasa don nuna fushinsu kan rashin tsaro a gabashin kasar.
Ana ci gaba da neman wata likita ‘yar kasar Poland da aka yi garkuwa da ita a kudancin kasar Chadi, kamar yadda jami'ai da kafafen yada labarai a kasar Poland suka ruwaito yau Litinin.
Adadin wadanda suka mutu sakamakon zaftarewar kasa da ta afku a wani kauye inda ake hakar zinari a kudancin kasar a cewar hukumomin kasar.
Ministar kasuwanci ta Burtaniya, Kemi Badenoch ta isa Najeriya domin fara ziyarar aiki ta kwanaki uku, da nufin zurfafa hadin gwiwa tsakanin Burtaniya da Najeriya.
A Alhamis din nan Alkalan Kotun Kolin Amurka suka tsinci kawunansu a wani hali na tababa dangane da hukunci akan batun haramtawa tsohon Shugaban Kasar Amurka, Donal Trump shiga zaben fidda gwanin jam'iyyarsa a jihar Colorado
Wani jami'in shari'ar kasar Tunisia ya sanar a ranar Alhamis cewa an gano gawarwakin 'yan ci-rani 13 'yan kasar Sudan, yayin da wasu 27 suka bace bayan wani jirgin ruwa ya nutse a ranar Laraba a gabar tekun Tunisiya bayan da ya taso daga Sfax.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.