Isra'ila da Hamas na ci gaba da tattaunawa kan samun yarjejeniyar da ke da nufin samun tsagaita wuta da kuma 'yantar da mutanen da aka yi garkuwa da su a zirin Gaza, a cewar jami'ai biyu da ke da masaniya kai tsaye kan tattaunawar.
Shugaban Amurka Joe Biden ya shiga TikTok a ranar Lahadin da ta gabata, inda a karon farko ya wallafa wani bidiyo na dakika 26 a kafar sada zumuntar ta Tiktok.
'Yan sanda a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango sun harba barkonon tsohuwa a ranar Litinin don tarwatsa masu zanga-zangar da suka kona tayoyi da tutocin Amurka da na Belgium a kusa da ofisoshin jakadancin kasashen Yamma da na MDD a birnin Kinshasa don nuna fushinsu kan rashin tsaro a gabashin kasar.
Ana ci gaba da neman wata likita ‘yar kasar Poland da aka yi garkuwa da ita a kudancin kasar Chadi, kamar yadda jami'ai da kafafen yada labarai a kasar Poland suka ruwaito yau Litinin.
Adadin wadanda suka mutu sakamakon zaftarewar kasa da ta afku a wani kauye inda ake hakar zinari a kudancin kasar a cewar hukumomin kasar.
Ministar kasuwanci ta Burtaniya, Kemi Badenoch ta isa Najeriya domin fara ziyarar aiki ta kwanaki uku, da nufin zurfafa hadin gwiwa tsakanin Burtaniya da Najeriya.
A Alhamis din nan Alkalan Kotun Kolin Amurka suka tsinci kawunansu a wani hali na tababa dangane da hukunci akan batun haramtawa tsohon Shugaban Kasar Amurka, Donal Trump shiga zaben fidda gwanin jam'iyyarsa a jihar Colorado
Wani jami'in shari'ar kasar Tunisia ya sanar a ranar Alhamis cewa an gano gawarwakin 'yan ci-rani 13 'yan kasar Sudan, yayin da wasu 27 suka bace bayan wani jirgin ruwa ya nutse a ranar Laraba a gabar tekun Tunisiya bayan da ya taso daga Sfax.
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya yi watsi da bukatar kungiyar Hamas na tsagaita wuta tare da ba da umarni ga sojojin kasar da su shirya kutsawa birnin Rafah da ke kudancin Gaza, inda Falasdinawa sama da miliyan daya suka nemi mafaka.
Wasu fashe-fashe guda biyu a kusa da ofisoshin 'yan takara a lardin Balochistan na kudu maso yammacin Pakistan sun kashe mutane 26 tare da jikkata wasu da dama, a cewar jami'an yankin a ranar Laraba 7 ga watan Fabrairu, lamarin da ya kara nuna damuwa kan tsaro a jajibirin babban zabe.
Hamas ta gabatar da shirin tsagaita wuta da a zirin Gaza na tsawon watanni hudu da rabi, inda duk wadanda aka yi garkuwa da su za su kubuta, Isra'ila kuma za ta janye sojojinta daga zirin Gaza sannan kuma za a cimma yarjejeniya kan kawo karshen yakin.
A jiya litinin masarautar Buckingham ta bayyana cewa, Sarki Charles na 3 ya kamu da cutar sankara kuma tuni ya fara karbar magani, duk da dai masarautar bata bayyana ko wacce irin sankara sabon Sarkin Ingilan ya kamu da ita ba.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.