Duk Litinin ta uku a watan Fabrairu, Amurkawa na gudanar da bukin ranar Shugaban Kasa.
Jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya Linda Thomas-Greenfield, ta ce Amurka ba za ta goyi bayan kudurin ba a yadda aka tsara shi.
'Yan sandan Papua New Guinea sun ce mutane 53 ne aka kashe a wani rikicin kabilanci a yankin tsaunukan kasar da ke fama da rikice-rikice, wannan shi ne kisan kiyashi na baya-baya da aka gani mai alaka da dadaddiyar takaddama a yankin.
A wani hukuncin da ake ganin ya na iya lahani ga harkokin kasuwancin tsohon Shugaban Amurka, Donald Trump, an ci shi tarar kudi mai yawa a birnin New York baya ga takunkumin kasuwanci da aka kakaba ma shi.
Masar na shirin shirya wani yanki a kan iyakar Gaza wanda zai iya daukar Falasdinawa idan har hare-haren Isra'ila a kan Rafah ya yi sanadin 'yan gudun hijirar zuwa kan iyaka, in ji majiyoyi hudu, a wani mataki da suka bayyana a matsayin wani yunkuri na gaggawa da birnin Alkahira ke shiryawa.
Hukumar kula da gidajen yari a Rasha ta fada a wata sanarwa cewa Navalny ya kamu da rashin lafiya bayan da ya dawo daga wani dan tattaki da ya yi don mike kafa, inda daga baya ya yanke jiki ya fadi.
Houthis na kasar Yemen da ke samun goyon bayan Iran, za su ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwa na tekun Bahar Rum domin nuna goyon bayansu ga Falasdinawa muddin Isra'ila ta ci gaba da aikata laifuka a kansu, in ji shugabansu a ranar Alhamis.
A jiya laraba Amurka ta dorawa wasu mutane 3 da kamfanoni 4 takunkumi a sassan kasashen Iran, da hadaddiyar daular larabawa da Turkiyya, bisa dalilin zargin su da taimakawa wajen fitar da kayayyaki, da sayen fasahohi daga kamfanonin Amurka zuwa kasar Iran da babban bankin kasar.
Wani kwale-kwalen da ke dauke da bakin haure ya kife a gabar tekun Caribbean na Panama kusa da dajin Darien, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da ba a san adadinsu ba, kamar yadda hukumomin kasar suka fada jiya Laraba.
Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan a ranar Laraba ya kai ziyararsa ta farko a Masar tun shekara ta 2012, inda ya gana da Shugaba Abdel Fattah al-Sisi
Tarayyar Turai EU, ta kudiri aniyar sake daura damara da ganin an sake tsugunar da tubabbun mayakan Boko Haram a kasashen yankin tafkin Chadi domin aiwatar da cikakken zaman lafiya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.