A Alhamis din nan Alkalan Kotun Kolin Amurka suka tsinci kawunansu a wani hali na tababa dangane da hukunci akan batun haramtawa tsohon Shugaban Kasar Amurka, Donal Trump shiga zaben fidda gwanin jam'iyyarsa a jihar Colorado
Wani jami'in shari'ar kasar Tunisia ya sanar a ranar Alhamis cewa an gano gawarwakin 'yan ci-rani 13 'yan kasar Sudan, yayin da wasu 27 suka bace bayan wani jirgin ruwa ya nutse a ranar Laraba a gabar tekun Tunisiya bayan da ya taso daga Sfax.
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya yi watsi da bukatar kungiyar Hamas na tsagaita wuta tare da ba da umarni ga sojojin kasar da su shirya kutsawa birnin Rafah da ke kudancin Gaza, inda Falasdinawa sama da miliyan daya suka nemi mafaka.
Wasu fashe-fashe guda biyu a kusa da ofisoshin 'yan takara a lardin Balochistan na kudu maso yammacin Pakistan sun kashe mutane 26 tare da jikkata wasu da dama, a cewar jami'an yankin a ranar Laraba 7 ga watan Fabrairu, lamarin da ya kara nuna damuwa kan tsaro a jajibirin babban zabe.
Hamas ta gabatar da shirin tsagaita wuta da a zirin Gaza na tsawon watanni hudu da rabi, inda duk wadanda aka yi garkuwa da su za su kubuta, Isra'ila kuma za ta janye sojojinta daga zirin Gaza sannan kuma za a cimma yarjejeniya kan kawo karshen yakin.
A jiya litinin masarautar Buckingham ta bayyana cewa, Sarki Charles na 3 ya kamu da cutar sankara kuma tuni ya fara karbar magani, duk da dai masarautar bata bayyana ko wacce irin sankara sabon Sarkin Ingilan ya kamu da ita ba.
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya isa Saudiyya a yau Litinin a ziyararsa ta biyar a yankin tun bayan barkewar yaki a yankin Gaza, yana fatan ci gaba da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma shiri bayan yakin da dakile tashe-tashen hankula a yankin.
Wata takardar babban bankin kasar da wani jami’i a bankin ya tabbatar da sahihancinta ce ta bayyana sunayen bankunan da aka haramtawa amfani da dalar.
Tsohon gwamnan jihar Yobe Sanata Bukar Abba Ibrahim ya rasu yana da mai shekaru 75.
Isra'ila ta yi watsi da hukuncin da babbar kotun Majalisar Dinkin Duniya ta yanke a makon da ya gabata, ta hanyar kashe daruruwan fararen hula a Gaza 'yan kwanaki bayan yanke hukumcin, kamar yadda Ministar harkokin wajen Afirka ta Kudu ta fada jiya Laraba,
Wata kotun yaki da cin hanci da rashawa a Pakistan ta yanke hukuncin daure Imran Khan da matarsa Bushra Khan na tsawon shekaru 14 kowannensu, bisa zargin sayar da kyaututtukan gwamnati ba bisa ka'ida ba, jam'iyyarsa ta ce a yau, Laraba.
Kamfanin dillancin labarai na Yonhap ya bayar da rahoton cewa, a ranar Laraba ne wata kotu a Koriya ta Kudu ta yanke hukuncin daurin rai da rai ga mutumin da ya kashe mutum daya tare da jikkata wasu uku a wani hari da aka kai a birnin Seoul a bara.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.