Yayin da Janhuriyar Nijar ke dada daukar tsauraran matakai kan harkokin shigi da fici, ta na kuma sassauta ma bakin da ke cikin kasar
Shugaba Tinubu ya rushe majalisar gudanarwar jami’ar tare da sauke Farfesa Aisha Sani Maikudi daga kan mukaminta na shugabancin Jami’ar Yakubu Gowon.
Mataimakin Kakakin Majalisar Benjamin Kalu wanda ya jagoranci zaman majalisar na yau Alhamis ne ya karanta wasikar da ta fito daga kwamitin da ke dauke da sunayen jihohin da aka ba da shawarar kirkirar.
Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan fashin daji ne sun sace tsohon babban daraktan hukumar kula da matasa ‘yan hidimar kasa a Najeriya (NYSC), Manjo Janar Mahrazu Tsiga (mai ritaya).
Yankin Arewa Maso Tsakiyar Najeriya ya samu hukumar kulawa da matsalolinsa kamar yadda yankunan Naija Delta da Arewa maso Gabas ke da nasu.
A cewar Onanuga, ziyarar shugaban zuwa kasar da ke nahiyar Turai ta kashin kai ce, inda ya kara da cewa Tinubu zai yi ziyarar ne a kan hanyarsa ta zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha
Karin kasafin kudin ya samo asali ne sakamakon samun karin kudin shiga na Naira tiriliyan 1. 4 daga hukumar tara kudaden shiga ta Najeriya (FIRS), da Naira tiriliyan 1.2 daga hukumar yaki da fasakwabrin kasar (NCS) da kuma Naira tiriliyan 1.8 da sauran hukumomin gwamnati suka tara.
Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara wadda ta tabbatar da faruwar Lamarin ta bakin jami’in hulda da jama’a na Rundunar DSP Yazid Abubakar yace mutane 17 ne suka mutu yayin da wasu 17 suke kwance a asibiti suna samun kulawar likitoci.
Duk da jinkirta matakin a wasu fannoni, har yanzu akwai fargaba akan abin da zai kasance nan gaba a bangaren tallafin da Amurka ke bayarwa a fannin lafiya a fadin duniya.
Domin Kari
No media source currently available