Masana sun bayyana mata da ke kai harin kunar bakin wake a matsayin makaman ‘yan ta’adda na boye, kasancewa ba a zaton za su iya kai irin wannan harin.
“Duba da cewa jirgi ne mara matuki, ba a samu wani da ya mutu ko ya ji rauni ba.” In ji wata sanarwa da darektan yada labarai, Air Vice marshal Edward Gabkwet ya wallafa a shafin Facebook na rundunar.
Gwamnatin jihar Legas ta kuma ba da sanarwar samun gagarumar raguwar yawan mutanen da ke kamuwa da kwalarar a kowace rana.
A cewar Kwamandan Shiyyar Kano na Hukumar FRSC, “binciken farko ya nuna akwai yiyuwar cewar tsananin gudu ne ya sa tirelar ta kwace daga hannun direbanta”.
Mai Shari’a Omotosho, yace Kanu ya gaza gabatar da gamsassun hujjojin da zasu tabbatar da ikirarinsa na hana shi ganawa da lauyoyinsa ba tare da tarnaki ba.
“Na dawo gare ku masu murna, masu farin ciki, ina mamakin ku, kuma ina takaicin wannan dabi’a ta ku, saboda ba dabi’a ba ce mai kyau." In ji Aisha.
Jami’ar hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Omolola Odutola, ta tabbatar da sace wani direba da wasu mutane dauke da makamai suka yi a hanyar Ijebuode/Sagamu.
A cewar kwamishinan, mai yiwuwa maharan sun yi amfani ne da kan iyakokin jihar da babu tsaro wajen kai hare-haren.
Yankin kauyen na Tiami da jirgin ya fadi ba shi da tazara mai nisa daga hedkwatar horar da matuka jirgin saman sojin Najeriya da ke yankin Mando a karamar hukumar ta Igabi.
Shugaba Bola Tinubu ya yi Allah-wadai da harin kunar bakin wake da aka kai ranar Asabar a jihar Borno da ya bayyana matsayin ta'addanci, yayinda gwamnatin Amurka ta bayyana niyar hada hannu da gwamnatin Najeriya wajen yaki da ta'addanci.
An kasha akalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan kunar bakin wake ne suka kai a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.
Domin Kari
No media source currently available