Jami'an Amurka sun ce suna aiki ta hanyar diflomasiyya don ganin an kawar da barkewar mummunan fada tsakanin Isra'ila da mayakan Hezbollah masu samun goyon bayan Iran da ke kudancin Lebanon.
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya rattaba hannu kan wasu jerin yarjeniyoyi da takwaransa na kasar Vietnam To Lam a yau Alhamis, yayin wata ziyarar aiki da ya kai kasar a daidai lokacin da Moscow ke neman karfafa alaka a nahiyar Asiya.
Guguwar da aka yi mata lakabin Alberto ta yi kaca-kaca da arewa maso gabashin Mexico da sanyin safiyar Alhamis a matsayin guguwar farko da aka ambata a kakar bana, dauke da ruwan sama mai karfi da ya yi sanadin mutuwar mutane uku, amma ya kawo jimami mai kyau ga yankin mai fama da matsanancin fari
Akalla mutane biyu ne suka mutu yayin da wasu tara suka jikkata yau Alhamis a lokacin da wani jirgin kasa dauke da fasinjoji ya yi ci karo da wani jirgin kasa mai gwajin aiki a babban birnin kasar Chile, Santiago.
Ministan kula da Ma'adanai na Nijar ya bai wa kamfanin ORANO da ke aikin hakar ma'adanin Uranium a kasar wa'adin kwanaki uku ko ya fara aiki ko kuma a soke lasisinsa
A ranar Larabar nan ne Indiya ta yi fama da matsanancin yanayi da ya haifar da tsananin zafi da zabtarewar kasa da kuma ambaliyar ruwa.
Wani babban jirgin ruwan dakon kaya ya nutse 'yan kwanaki bayan wani harin da 'yan tawayen Houthi na Yaman suka kai masa, kuma ana kyautata zaton harin ya kashe wani mutum a cikin jirgin, a cewar hukumomi da safiyar Laraba, wanda shi ne jirgi na biyu da ya nutse sanadiyyar hare haren 'yan tawayen.
Shugabannin kasashen Koriya ta Arewa da na Rasha sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya a ranar Larabar nan, wadda ta kara zurfafa hadin gwiwarsu ta soji, da ta hada da alkawarin kare juna, na taimakon juna idan har aka kai wa daya hari, inda Kim Jong Un na Arewa ya kira sabuwar alakar da "kawance".
Daruruwan mahajjata ne suka mutu bana a yayin gudanar da aikin hajjin shekara-shekara da Musulmi ke gudanarwa a Makka sanadiyar tsananin zafi, kamar yadda rahotannin manema labarai da ma'aikatun harkokin waje suka bayyana.
Wakilan Sudan sun zargi Hadaddiyar daular larabawa da taimaka wa dakarun RSF ta hannun mayakan sa-kai dake Chadi, kudancin Libya da kuma birnin Khartoum.
Shugaba Joe Biden ya sanar da wani sabon tsari da zai ba wadanda su ka auri Amurkawa, da kuma 'ya'yan mutanen da su ka auri Amurkawa, izinin zama kasar din-din-din.
Hare-haren da Isra'ila ta kai ta sama a ranar Talata sun hallaka akalla Falasdinawa a wasu sansanonin zirin gaza 2 masu tarihi, a yayin da tankokin Isra'ila ke kara kutsawa zuwa kudancin birnin Rafah, a cewar mazauna yankin da ma'aikatan lafiya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.