'Yan sandan kasar Brazil da ke bincike kan gano wani karamin jirgin ruwa cike da gawarwaki sun ce akwai yiwuwar gawarwakin na 'yan ci-rani ne daga kasashen Mali da Mauritania a nahiyar Afrika.
Shugabannin duniya sun bukaci Isra'ila da kada ta mayar da martani bayan da Iran ta kai harin da ya hada da daruruwan jirage marasa matuka, da makamai masu linzami da kuma sauran makamai.
Manyan jami'an diflomasiyya da kungiyoyin agaji sun yi taro ranar Litinin a birnin Paris, domin bullo da hanyoyi na taimakon jin kai ga kasar Sudan da ke arewa maso gabashin Afirka, wadda ke daf da fuskantar matsananciyar yunwa, domin gudun sake fadawa cikin mawuyacin hali.
Iran ta harba jirage marasa matuka masu tarwatsewa tare da harba makamai masu linzami kan Isra'ila da yammacin jiya Asabar - harin da ta kai na farko kai tsaye a kan yankin Isra'ila a matsayin ramuwar gayya da ke kara tsananin barazana a rikicin yankin.
Mai magana da yawun fadar White House a fannin tsaro, John Kirby ya shaidawa gidan talabijin din CNN cewa "galibin makaman da aka harba ta sama, daga Iran aka harba su.
Jiragen Iran marasa matuka sun nufi Isra'ila, in ji Press TV na kasar Iran mai yada labarai da harshen Ingilishi, yayin da ya ambato majiyoyin Iran.
Jiragen saman Isra'ila sun kashe 'ya'yan babban jagoran siyasar Hamas guda uku a zirin Gaza a jiya Laraba, a daidai lokacin da Isra'ila ke gudanar da tattaunawar tsagaita bude wuta da kungiyar ta Hamas.
Ministan harkokin cikin gida na kasar Turkiyya ya ce ‘yan sanda sun kama hodar ibilis mafi girma na uku a tarihin kasar.
Kasar Sin ta sanar da sanya takunkumai da ba kasafai aka saba gani ba a kan wasu kamfanonin tsaron Amurka biyu, saboda abin da ta ce na goyon bayan sayar wa Taiwan makamai.
Mutane 9 da suka hada da jariri daya ne suka mutu bayan kifewar kwale-kwalen da suke cikin a lokacin da suke kokarin tsallakawa tekun Bahar Rum a cikin yanayi mai hadari, kuma ana fargabar bacewar wasu mtuane 15, kamar yadda ma’aikatan tsaron gabar ruwan Italiya suka sanar a yau Alhamis.
A yau Alhamis, sojojin Isira’ila sun sanar da abin da suka kira, sababbi matakai da aka inganta na shigar da kayan agaji zuwa zirin Gaza, cikin har da gina wata sabuwar mashiga ta kasa a arewacin Gaza.
A ranar Lahadin da ta gabata ne dan tsere Russ Cook ya isa yankin arewacin Afirka, kusan shekara guda bayan ya tashi daga kudancin nahiyar a yunkurinsa na kure tsawon nahiyar da gudu.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.