Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya na daga cikin jihohin da ke fama da matsalar barayin daji wadanda ke satar mutane don neman kudin fansa.
Isra’ila ta ce daya daga cikin hare-haren da ta kai a yankunan kudancin birnin Beirut ya kashe Ibrahim Muhammad Kobeisi, wanda Isra’ila ta bayyana a matsayin babban kwandan sojojin Hezbollah da ke sa ido kan tsarin makamai masu linzami na Hezbollah.
Yayin da yake jawabi a gaban taron, Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu ya ce, lokaci ya yi da za a sharewa Afirka hawayenta kan wannan bukata.
Al’amarin ya hada da wani kwale-kwale dake dauke da fasinjoji wanda ya nutse a cikin ruwan ambaliya, abinda yayi sanadiyar mutuwar wasu mata 4.
Ministan Tsaron Najeriya Abubakar Badaru ne ya gabatar da bukatar a taron kolin da aka yi kan makomar duniya yayin karo na 79 na babban taron zauren Majalisar Dinkin Duniya dake gudana a birnin New York, na Amurka.
A wata hira ta musamman da Bloomberg, hamshakin attajirin nan na Najeriya, Aliko Dangote, ya tattauna kalubale da matakan da suka dauka dangane da kaddamar da matatarsa, wadda ita ce mafi girma a Afirka.
Daga cikin wadanda aka kashe a hare-haren har da yara 35 da mata 58, a cewar jami'an Lafiyar Lebanon.
A ranar Lahadi, hukumar INEC ta ayyana dan takarar jam’iyyar APC Monday Okpebholo a matsayin wanda ya lashe zaben jihar ta Edo, nasarar da PDP ta ke kalubalanta.
“Ya kamata babbar jam’iyya kamar APC ta samu cikakken iko a shiyyar Kudu Maso Gabas,” in ji Ganduje, inda ya bukaci shugabannin jam’iyyar da su kara zage damtse don tabbatar da mulkin APC a yankin.
Bayanan da aka samu daga babban bankin Najeriya (CBN) sun nuna cewa daga ranar 18 ga watan Satumbar da muke ciki, kudaden ajiyar Najeriya na ketare sun kai mizanin da rabon da aga irin haka tun ranar 4 ga watan Nuwambar 2022, lokacin da suka kai dala biliyan 37.36.
Dalibai da ma’aikatan jami’ar tarayya ta Gusau a jihar Zamfara, wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa dasu, sun shaki iskar ‘yanci bayan shafe watannin 7 a hannunsu.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.