Ma'aikatar Jinkai da Rage radaddin talauci ta ce ta samu wasu makudan kudade a binciken da ta ke gudanarwa, saboda haka ta shirya biyan 'YAN BATCH C' wadanda ke bin bashin alawus din su har na tsawon wattani 9.
Ma'aikatan hukumar yi wa kamfanoni rajista ta Najeriya "Corporate Affairs Commission" sun yi gangamin nuna farin cikin rashin sabuntawa shugaban hukumar Barista Garba Abubakar sabon wa'adi bayan shafe shekara uku da wata tara kan kujera.
Hedkwatar rundunar sojojin saman Najeriya ta yi karin haske kan wasu tagwayen hare-hare da jiragen yakinta su ka kai kan gungun wasu yan bindiga a kan iyakokar jihohin kebbi da zamfara.
A ranar Litinin ne shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da karin ministoci uku da majalisar dattawan kasar ta tantance da su kwanan nan.
Gwamnatin jihar Filato da ke arewa ta tsakiyar Najeriya ta soma wani yunkuri domin ganin jama’ar jihar sun amfana da ilmi, arziki, wayewa da fasahar ‘yan asalin jihar da ke zaune a Amurka da ma sauran kasashen duniya.
Masu ruwa da tsaki a jihar Nasarawan Najeriya sun yi kira ga al’ummar jihar da su maida wukakensu cikin kube, bayan musayar kalamai daga magoya bayan jami’iyyar APC da PDP a jihar, biyo bayan hukuncin da kotun sauraren kararrakin zabe ta yanke.
Farashin litar man fetur kan iya karuwa a ko yaushe; hakanan ba mamaki a wayi gari da dogayen layukan neman fetur don barin kasuwa ta daidaita kanta.
Yayin da aka shiga mako na 2 da barkewar sabon fada tsakanin Isra’ila da Hamas, Zauren Malaman Addinin Musulunci na Najeriya ya bayyana rashin jin dadi kan abubuwan dake faruwa a can, a hannu guda kuma masana sun ce rashin mutunta kudurorin majalisar dinkin duniya suka sa yakin ke ci gaba da faruwa.
Majalisar Dattawan Najeriya ta yi kwaskwarima ga dokar hukumar kula da Zuba Jari ta kasa wacce aka fi sani da NSIP, da nufin dauke hukumar daga ma'aikatar agaji da rage talauci zuwa fadar shugaban kasa. Amma kwararre a fannin zamantakewar bil'adama na ganin abin ba zai canja zani ba.
Jiragen yakin sojin Najeriya sun kai farmaki ta sama kan wani dandazon ‘yan bindiga, inda suka kashe ‘yan bindiga kusan 100 a yankin arewa maso yammacin kasar.
Yankin na Gaza na karkashin kawanyar Isra’ila, wani mataki da Isra'ilan ta dauka a matsayin martanin mummunan harin da Hamas ta kai wa Isra’ilan a ranar Asabar din da ta gabata, wanda ya halaka daruruwan fararen hula.
Rundunar tsaron kasar ta ce sun kuma cafke karin wasu ‘yan ta’adda guda dari da goma sha hudu.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.