Majalisar Dattawan Najeriya ta yi kwaskwarima ga dokar hukumar kula da Zuba Jari ta kasa wacce aka fi sani da NSIP, da nufin dauke hukumar daga ma'aikatar agaji da rage talauci zuwa fadar shugaban kasa. Amma kwararre a fannin zamantakewar bil'adama na ganin abin ba zai canja zani ba.
Jiragen yakin sojin Najeriya sun kai farmaki ta sama kan wani dandazon ‘yan bindiga, inda suka kashe ‘yan bindiga kusan 100 a yankin arewa maso yammacin kasar.
Yankin na Gaza na karkashin kawanyar Isra’ila, wani mataki da Isra'ilan ta dauka a matsayin martanin mummunan harin da Hamas ta kai wa Isra’ilan a ranar Asabar din da ta gabata, wanda ya halaka daruruwan fararen hula.
Rundunar tsaron kasar ta ce sun kuma cafke karin wasu ‘yan ta’adda guda dari da goma sha hudu.
A yayin da ‘yan Najeriya ke fama da tsadar kayayyakin da suka shafi makamashi kamar iskar gas, man fetur da wutar lantarki, tare da hauhawar farashin da ake samu kusan kullum, gwamnatin kasar ta ce za’a sami walwala nan ba da jimawa ba.
Gwamnatin ta Najeriya ta dakatar da Ziyarar ne har sai an samu salama, biyo bayan kaurewar fada tsakanin Falasdinawa ‘yan kungiyar Hamas da sojojin Isra’ila.
A yayin da ake murnar zagayowar ranar ‘ya’ya mata ta duniya, iyaye mata, dalibai, malamai da wasu masu ruwa da tsaki sun sake jaddada mahimmancin bai wa ‘ya’ya mata irin damammakin da ake bai wa takwarorinsu maza.
Masana sun bayyana cewa rikicin Isra’ila da Hamas ka iya sa ‘yan Najeriya fuskantar kalubale wajen sayen man fetur duk da cewa an sami hauhawar farashin man fetur a duniya, lamarin da ya kamata a ce ya taimaka wa masana’antar danyen mai ta kasar.
Hukumar kula da lafiya ta duniya ta ware ranar 10 ga watan Oktoba na kowace shekara a matsayin ranar kula da lafiyar kwakwalwa ta duniya domin wayar da kan al’umma kan abunda suka shafi kula da lafiyar kwakwalwa.
Wasu ‘yan bindiga a Najeriya sun yi garkuwa da mutane hudu a wani gida a garin Keffi da ke jami’ar jihar Nasarawa ta yankin tsakiyar Najeriya, kamar yadda ‘yan sanda suka bayyana a ranar Talata.
Ganin cewa rikicin na gabas ta tsakiya sai ƙara rincaɓewa yake yi, masana a Najeriya sun yi kira ga shugabanin Afirka da su yi azama wajen ganin cewa an kawo ƙarshen rikicin ba da daɗewa ba.
“Hukumar za ta sanar da sabon lokacin da za a ci gaba da jigilar masu zuwa ibada a zango na biyu.” Sanarwar hukumar ta ce.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.