A ranar Talata kungiyar ta Hamas ta sanar da nada Yahya Sinwar a matsayin sabon shugabanta bayan kisan Isma'il Haniyeh a Iran da ake zargin Isra'ila na da hannu.
Da alama wata makarmashiyar Iran ta kashe tsohon Shugaban Amurka Donald Trump na da nasaba da yunkurin wani dan Pakistan mai alaka da Tehran na niyar kaiwa wasu manyan 'yan siyasa da jami'an Amurka hari.
An sake zaben Walz a wa’adi na biyu a shekarar 2022 a jihar ta Minessota bayan da ya doke dan takarar jam'iyyar Republican Scott Jensen.
Walz, wanda Gwamna ne mai ci kuma tsohon soja, ya taka muhimmiyar rawa wajen kare ‘yancin zubar da ciki a Amurka.
Kasuwannin hannayen jari a fadin duniya na tangal tangal, yayin da ake fargabar tsunduma cikin matsalar tsananin tsadar kaya musamman ma a manyan kasashe irin Amurka da Japan da sauransu
Shugaban Amurka Joe Biden ya jaddada cewa fito da Amurkawa da sauran ‘yan wasu kasashen daga gidajen yarin Rasha wata babbar nasarace ta bangaren diflomasiyya da kawance.
Cibiyar Kula da Cututtuka Masu Yaduwa ta Amurka ta fada a ranar Talata cewa, tana shirin kashe dala miliyan 10 don dakile kamuwa da cutar murar tsuntsaye tsakanin ma’aikatan gona, da ya hada da dala miliyan 5 don rigakafin mura na lokaci-lokaci.
Akalla yara ‘yan asalin Amurka 973 ne suka mutu a tsarin makarantun kwana na gwamnatin Amurka inda ake cin zarafin yaran, bisa ga sakamakon wani bincike da jami’ai suka fitar jiya talata da suka yi kira ga gwamnati da ta sa makarantun sun nemi afuwar daliban.
Amurka da Birtaniya da kuma Canada sun fitar da sanarwar gargadi ga ‘yan kasashensu mazauna a Najeriya, kan su zauna cikin shiri kan yiwuwar barkewar rikici yayin zanga-zangar da aka shirya za a yi a kasar.
Ta yiwu abokan hamayya a zaben Amurka da ke tafe, mataimakiyar shugaban kasar Kamala Harris da tsohon shugaba Donald Trump sun bayyana mabambantan ra'ayoyi game da yadda Isra'ila ke yin yaki a Gaza, a lokacin da suka gana da Firai Minista Benjamin Netanyahu a lokuta dabam dabam a wannan makon.
A yau Juma’a, tsohon shugaban Amurka Barack Obama da mai dakinsa Michelle sun bayyana goyon bayansu ga Mataimakiyar Shugaban Kasa Kamala Harris a matsayin wacce za ta yi wa jam’iyyar Democrat takarar shugaban kasa.
Zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da Firai ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ke kare yakin da kasar ke yi a Gaza, a yayin jawabi da ya yi a zauren Majalisar dokokin Amurka.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.