Sabuwar tuhumar ta cire batun zargin tattaunawa da aka ce Trump ya yi da Ma’aikatar Shari’a.
Wannan shi ne karo na farko da Harris za ta zanta da wata kafar yada labarai tun bayan da ta maye gurbin Shugaba Joe Biden wanda ya janye takararsa.
Wan Mai Shari’a A Amurka Ya Dakatar Da Shirin Da Ke Baiwa Iyalan Amurkawa Iziznin Zama 'yan Kasa
Tallan yunkuri ne na jan hankalin masu kada kuri’a a jihohin da ke da muhimmanci wajen samun kuri’u wadanda suka hada da Arizona da Nevada.
Gabbard ita ce ‘yar majalisar daya tilo da ta ki kada kuri’a a lokacin da majalisar wakilai ta tsige Trump saboda wasu huldodi da ya yi da Ukraine.
Mataimakiyar Shugaban kasa Kamala Harris ta ce yakin neman zabenta ya tara dala miliyan 540 ya zuwa yanzu kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AP ya ruwaito.
Mataimakiyar shugaban Amurka, Kamala harris, ta yi kira ga Amurkawa da su hada kai da a ranar Alhamis, yayin da take amincewa da zabenta da aka yi a matsayin ‘yar takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar Democrat.
Kusoshin jam'iyyar Democrat da dama sun yi jawabai a rana ta uku a babban taron kasa na jam'iyyarsu wanda ke gudana a birnin Chicago na jahar Illinois ta Amurka
A daren jiya an shiga babi na farko na daya daga cikin rukunoni mafiya muhimmanci na wannan taron, wato kiran ‘yan deliget daga jihohin Amurka, su yi shelar kada kuri’unsu ga ‘yar takarar shugaban kasa a jam’iyyar ta Democrat, Mataimakiyar Shugaban kasa, Kamala Harris.
Barack Obama ya gabatar da jawabi mai karfafa zuciya da kyakyawar fata akan takarar mataimakiyar shugaban Amurka Kamala Harris.
A babban taron jam’iyyar Democrats na kasa da aka fara jiya Litinin, wakilai sun amince da takarar jam’iyyar na wannan shekarar ta 2024.
Ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta amince Amurka ta saida wa KTK jirage masu saukar ungulu da farashin shu ya kai dala biliyan $3.5.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.