Cibiyar Kula da Cututtuka Masu Yaduwa ta Amurka ta fada a ranar Talata cewa, tana shirin kashe dala miliyan 10 don dakile kamuwa da cutar murar tsuntsaye tsakanin ma’aikatan gona, da ya hada da dala miliyan 5 don rigakafin mura na lokaci-lokaci.
Akalla yara ‘yan asalin Amurka 973 ne suka mutu a tsarin makarantun kwana na gwamnatin Amurka inda ake cin zarafin yaran, bisa ga sakamakon wani bincike da jami’ai suka fitar jiya talata da suka yi kira ga gwamnati da ta sa makarantun sun nemi afuwar daliban.
Amurka da Birtaniya da kuma Canada sun fitar da sanarwar gargadi ga ‘yan kasashensu mazauna a Najeriya, kan su zauna cikin shiri kan yiwuwar barkewar rikici yayin zanga-zangar da aka shirya za a yi a kasar.
Ta yiwu abokan hamayya a zaben Amurka da ke tafe, mataimakiyar shugaban kasar Kamala Harris da tsohon shugaba Donald Trump sun bayyana mabambantan ra'ayoyi game da yadda Isra'ila ke yin yaki a Gaza, a lokacin da suka gana da Firai Minista Benjamin Netanyahu a lokuta dabam dabam a wannan makon.
A yau Juma’a, tsohon shugaban Amurka Barack Obama da mai dakinsa Michelle sun bayyana goyon bayansu ga Mataimakiyar Shugaban Kasa Kamala Harris a matsayin wacce za ta yi wa jam’iyyar Democrat takarar shugaban kasa.
Zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da Firai ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ke kare yakin da kasar ke yi a Gaza, a yayin jawabi da ya yi a zauren Majalisar dokokin Amurka.
Shugaba Joe Biden ya janye daga takarar ci gaba da zama a fadar White House sannan a maimakon hakan ya bayyana goyon bayansa ga mataimakiyarsa, Kamala Harris.
Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu zai samu tarba daga ‘yan Majalisar Dokokin Amurka dake fama da mummunan rabuwar kai da al’ummar kasar da suka shagaltu da wasu al’amura da kuma gagarumin gangamin zanga-zanga a yau Laraba yayin gabatar da jawabi gaban majalisar a karo na 4 a tarihi
Daraktar hukumar leken asiri ta Amurka, Kimberly Cheatle ta yi murabus daga aikinta, a cewar sakon imel da ta aike wa ma'aikatanta a yau Talata
Mataimakiyar Shugaban Amurka Kamala Harris ta samu goyon bayan wadatattun wakilan jam’iyyar Democrats domin zama wacce zata kara da Donald Trump 'dan Republican, a cewar binciken da kamfanin dillancin labarai na AP ya gudanar, kasancewar jiga-jigan ‘yan Democrats na mara mata baya.
A jiya Litinin ‘yan majalisar dokokin Amurka daga bangarorin biyu suka yi kira ga Daraktar hukumar tsaron farin kaya ta Amurka Kimberly Cheatle da ta yi murabus, yayin da take ba da shaida kan gazawar hukumar wajen hana yunkurin kashe dan takarar Shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donald Trump.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.