A daren jiya an shiga babi na farko na daya daga cikin rukunoni mafiya muhimmanci na wannan taron, wato kiran ‘yan deliget daga jihohin Amurka, su yi shelar kada kuri’unsu ga ‘yar takarar shugaban kasa a jam’iyyar ta Democrat, Mataimakiyar Shugaban kasa, Kamala Harris.
Barack Obama ya gabatar da jawabi mai karfafa zuciya da kyakyawar fata akan takarar mataimakiyar shugaban Amurka Kamala Harris.
A babban taron jam’iyyar Democrats na kasa da aka fara jiya Litinin, wakilai sun amince da takarar jam’iyyar na wannan shekarar ta 2024.
Ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta amince Amurka ta saida wa KTK jirage masu saukar ungulu da farashin shu ya kai dala biliyan $3.5.
A daren Litinin Shugaba Joe Biden ya gabatar da nasa jawabin a gangamin wanda ake sa ran zai tabbatarwa da Kamala Harris tikitinta na tsaya wa jam’iyyar takara shugaban kasa a zaben 5 ga watan Nuwamba.
Alamu sun nuna cewa Biden ya dan zubar da hawaye a lokacin da ya hau dandamalin da ya yi jawabin inda aka kwashe sama da minti hudu ana sowa da nuna masa kyakkyawar tarba.
Jiga jigan 'yan jam'iyyar Democrat sun fara jawabai a babban taron jam'iyyar da za a shafe wajen mako guda ana yi a birnin Chicago na jahar Illinois ta nan Amurka.
Fitowa da yin jawabi ba zato ba tsammani da Mataimakiyar Shugaban Amurka kuma 'yar takarar shugaban kasa, Kamala Harris, ta yi a babban taron jam'iyyar Democrat na daya daga cikin jerin abubuwan da su ka burge jama'a a daren farko na taron na kusan mako guda.
Jam’iyyar Democrat ta fara babban taronta na kasa a ranar Litinin a Chicago inda ake sa ran kusan mutum 50,000 za su isa birnin.
Ofishin jakadancin China da ke Tokyo ne ya ba da wannan gargadin bayan wata ziyara da wasu gungun ‘yan majalisar dokokin Japan suka kai a kasar Taiwan a wannan makon, ciki har da tsohon ministan tsaro Shigeru Ishiba, dan takarar da ake hasashen zai iya zama Prime ministan kasar na gaba.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.