Ofishin jakadancin China da ke Tokyo ne ya ba da wannan gargadin bayan wata ziyara da wasu gungun ‘yan majalisar dokokin Japan suka kai a kasar Taiwan a wannan makon, ciki har da tsohon ministan tsaro Shigeru Ishiba, dan takarar da ake hasashen zai iya zama Prime ministan kasar na gaba.
Wani mai gabatar da kara ya ce an tuhumi wasu mutane biyar da ake zargi da hannu a mutuwar Matthew Perry sakamakon amfani da wani magani mai hadari da ake kira ketamine a bara, ciki har da mataimakin jarumin da kuma likitoci biyu.
Kamfanin manhajar Google ya ce wata kungiyar kasar Iran mai alaka da Dogarawan Juyin Juya Halin kasar, ta yi ta yinkurin yin kutse ga akwatin sakonnin intanet na mutane wajen 12, wadanda ke da alaka da Shugaban Amurka Joe Biden, da tsohon Shugaba Donald Trump, tun daga watan Mayu.
A ci gaba da gano abubuwan al'ajibi da masu ilimin kimiyya ke yi, sun gano cewa ga dukkan alamu akwai dinbin ruwa karkashin duniyar Mars.
Wannan shi ne na baya-bayan nan na abin da ofishin kare hakkin bil Adama na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana da "Hare-hare kan makarantu a wayance" na Isra'ila, tare da a kalla hare-hare 21, tun daga ranar 4 ga watan Yuli, inda kuma suka hallaka daruruwan mutane, ciki har da mata da kananan yara.
Dakarun Ukraine sun kai farmaki a yankunan kan iyakar da safiyar Talata, a wani hari da ya kasance mafi girma da samun nasara da Kyiv kai a cikin shekaru 2 da rabi na yakin.
Tallafin zai kumshi makamai da karin kayan aiki, wanda zai kasance kunshin tallafi na 10 da Amurka ta aika zuwa Ukraine, tun lokacin da shugaba Joe Biden ya rattaba hannu kan dokar tallafawa tsaron Ukraine a watan Afrilu.
A ranar Talata kungiyar ta Hamas ta sanar da nada Yahya Sinwar a matsayin sabon shugabanta bayan kisan Isma'il Haniyeh a Iran da ake zargin Isra'ila na da hannu.
Da alama wata makarmashiyar Iran ta kashe tsohon Shugaban Amurka Donald Trump na da nasaba da yunkurin wani dan Pakistan mai alaka da Tehran na niyar kaiwa wasu manyan 'yan siyasa da jami'an Amurka hari.
An sake zaben Walz a wa’adi na biyu a shekarar 2022 a jihar ta Minessota bayan da ya doke dan takarar jam'iyyar Republican Scott Jensen.
Walz, wanda Gwamna ne mai ci kuma tsohon soja, ya taka muhimmiyar rawa wajen kare ‘yancin zubar da ciki a Amurka.
Kasuwannin hannayen jari a fadin duniya na tangal tangal, yayin da ake fargabar tsunduma cikin matsalar tsananin tsadar kaya musamman ma a manyan kasashe irin Amurka da Japan da sauransu
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.