Ana ci gaba da nuna alhini dangane da rasuwar Mai Shari’a a kotun kolin Amurka Justice Ruth Bader Ginsburg, wacce ta rasu a ranar Juma’a tana mai shekara 87.
Sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo ya isa kasar Brazil ranar Juma’a, inda ya ziyarci cibiyar tantance ‘yan gudun hijirar kasar Venezuela, yayin da ya yi kira ga dimokaradiya da kuma shugaban kasa Nicolas Maduro ya sauka daga kan Mulki.
Alkali Ruth Ginsburg wadda ta dade a matsayin alkalin kotun Amurka ta rasu yau jumma'a bayan ta yi fama da rashin lafiya na tsawon lokaci.
Ma’aikatar harkokin kasuwancin Amurka ta ce za ta fitar da wani umurni a ranar Juma’a wanda zai hana jama’ar kasar sauke manhajojin WeChat da TikTok na kasar China.
Bayanan binciken sirri na nuni da cewa har yanzu Rasha na kokarin yin kutse da katsalandan domin sauya sakamakon zaben Amurka na shekara ta 2020, kamar yadda ta yi a zaben shekara ta 2016.
Sanadiyyar Dirowa da mahaukaciyar guguwar nan ta Sally ta yi a yankunan gabar teku musamman a jahar Alabama ta Amurka, mutane da dama sun rasa wutar lantarki baya ga wasu nau'ukan barna masu yawan gaske.
Kamar yadda tsirarun jinsi su ka fi Turawa kamuwa da cutar a Amurka a bangaren manya, a bangaren matasa ma haka abin ya ke, tsirarun jinsi sun fi kamuwa.
Akwai alamar mahaukaciyar guguwar nan ta Sally za ta janyo ambaliyar ruwa idan ta karasa dannowa zuwa gabar teku a yau Laraba a Amurka.
Jiya Talata shugaban shugaban Amurka Donald Trump ya jagoranci bukin rattaba hannu a fadar White House, na yarjejeniyar maido da hulda tsakanin kasar Isira’ila da kasashen Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain.
Gwamnatin Amurka ta dauki matakin tsabtace tsarin zaben Najeriya ta hanyar da zata shafi manyan ‘yan siyasa masu ikon fada a ji.
A wani al'amari mai cike da tarihi, wasu kasashen Larabawa biyu, wato da Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain, za su rattaba hannu kan yarjajjeniyar hulda da kasar Isira'ila.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.