Akwai alamar mahaukaciyar guguwar nan ta Sally za ta janyo ambaliyar ruwa idan ta karasa dannowa zuwa gabar teku a yau Laraba a Amurka.
Jiya Talata shugaban shugaban Amurka Donald Trump ya jagoranci bukin rattaba hannu a fadar White House, na yarjejeniyar maido da hulda tsakanin kasar Isira’ila da kasashen Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain.
Gwamnatin Amurka ta dauki matakin tsabtace tsarin zaben Najeriya ta hanyar da zata shafi manyan ‘yan siyasa masu ikon fada a ji.
A wani al'amari mai cike da tarihi, wasu kasashen Larabawa biyu, wato da Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain, za su rattaba hannu kan yarjajjeniyar hulda da kasar Isira'ila.
Shugaba Donald Trump da abokin karawarsa na jami’iyar Democrat Joe Biden sun bayyana mabanbanta ra’ayoyi a jiya Litinin a kan abin da ya tada gobarar daji mai tarihi da ta yi barna a yammacin Amurka da ta kasheakalla mutum 35.
Makwanni bakwai gabannin gudanar da zabe a Amurka, shugaba Donald Trump ya yi ikirarin cewa ya yi abin a zo a gani wajen yaki da annobar coronavirus da kuma dakile yawan mace-mace a kasar.
Shugaban Amurka Donald Trump ya ba da sanarwar cewa Daular Bahrain ta amince da Isra’ila a matsayin kasa, biyo bayan irin wannan yarjejeniya tsakanin Isra’ila da Hadaddiyar Daular Larabawa a watan da ya gabata.
Kamar yadda Amurkawa su ka saba kowace shekara, yau ma su na alhanin mutuwar mutane wajen 3000 a harin ta'addancin nan na ranar 11 ga watan Satumban 2001.
An dakatar da gwaje-gwajen maganin riga kafin COVID-19 na kamfanin AstraZeneca, abinda Dr. Fauci ya ce hakan ya nuna cewa ana kokarin tabbatar da ingancin magungunan.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.