Gwamnan Kaduna seneta Uba Sani ya ce “al’umma za su sake zaban APC a duk matakai daga sama har kasa. A can sama shine jagoran mu, shugaba Bola Ahmad Tinubu zai yi tazarce a zaben 2027. A matakin jiha kuma, jam’iyyar zata yi nasara, har da matakan majlisar tarayya da ta jihohi da izinin Allah.”