Jamhuriyar Nijar, Laraba 30 ga watan Nuwamba ake shagulgulan tunawa da ranar aikin ‘yan jarida ta kasa wacce ta samo asali a shekarar 2012 lokacin da shugaban kasa Mahamadou Issohou a zamaninsa ya saka hannu akan dokar hana kulle ‘dan jarida agidan yari saboda aikinsa.
Yayin da karancin alkama da yakin Ukraine ya haddasa ke ci gaba da janyo tsadar burodi da dangoginsa a sassan duniya, talakawa a Janhuriyar Nijar na ganin wani sa'in ana fakewa da yakin Ukraine ne a kuntata masu.
Shugabanin jam’iyyar PNDS Tarayya na kasashen yankin Kudanci da na tsakiyar Afurka sun gudanar da taro a birnin Yamai a jiya Asabar, wato wata daya kenan kafin a gudanar da babban taron jam’iyyar na kasa wanda zai bada damar zaben sabon shugaban jam’iyyar na kasa da mataimakansa.
Shugabanin kasashe da na gwamnatocin Afrika sun gudanar da taron wuni 1 a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijer.
Majalisar dokokin jamhuriyar Nijar ta karyata wasu bayanai da ke cewa ‘yan majalisar sun fara yunkurin kara wa kansu kudaden alawus-alawus duk da yanayin talauci da tsadar rayuwar da al’umma ke fuskanta, kuma a lokacin da matsalar tsaro ta addabi dubban ‘yan kasar a sassa da dama.
Gwamnatin rikon kwaryar Burkina Faso ta bayyana takaici a game da abinda ta kira halin ko in kular da wasu kasashe abokan kawancenta ke nuna mata dangane da halin tabarbarewar sha’anin tsaron da ta tsinci kanta ciki sakamakon aika - aikar ‘yan ta’adda yau shekaru a kalla 7.
Hukumomin Jamhuriyar Nijer sun kama wasu fitattun mawakan Najeriya lokacin da su ke kokarin hada takardu don samun fasfon kasar ta Nijer da nufin zuwa kasashen turai.
A wata hira da shugaban kungiyar makafi ya kwatanta girman wannan matsala da kuma hanyoyin da yake ganin idan aka bi su za a warware wannan kulli.
Shuwagabanin hukumomin yaki da cin hanci daga kasashen Afrika ta yamma suna gudanar da taron wuni 1 a birnin Yamai a karkashin inuwar kungiyarsu ta NACIWA ko RINLCAO.
Hukumar zaben Jamhuriyar Nijar ta yi bitar ayyukan rijistar da ta gudanar a watan Oktoban da ya gabata a wasu kasashen waje a ci gaba da shirye-shiryen zaben mutanen da za su wakilci ‘yan kasar ta Nijar mazauna ketare a majalissar dokoki.
Binciken da kungiyar ROTAB Niger ta ce ta gudanar a daukacin yankunan da ke da arzikin ma’adanai ya bada damar gano rashin adalcin da ake yi wa mata da yara a Nijar.
A cikin shirin na wannan makon mun duba halin da malaman ke ciki domin ba ya ga karancin kayan aiki, wadanan malamai na fatan ganin an bullo da hanyoyin ba su horo ta yadda za su sami kwarewar da ke daidai da ci gaban da zamani ya zo da shi don taimakawa daliban.
Taron hukumomi da kungiyoyin kasashen Afrika masu rajin kare hakkin dan Adam karo na 73 da ke gudana a kasar Gambia, ya yaba da yadda jamhuriyar Nijer ta maida hankali wajen mutunta wasu mahimman ‘yancin dan Adam.
Shugabannin hukumar kare hakkin dan adam ta CNDH sun kai ziyara a asibitocin da aka kwantar da mutanen da suka ji rauni a yayin ruwan wutar da jiragen sojan saman Nijar suka yi.
An kafa makarantar ne a wani bangare na matakan shigar da nakasassu a sha’anin ilimin boko ta yadda za su tashi da tunanin rungumar kwakkwarar madogarar rayuwa a maimakon shiga harakar bara.
Hukumomin Nijer sun fara nazarin sabbin hanyoyin magance matsalar bara bayan la’akari da yadda wasu ‘yan kasar dauke da yara kanana ke kwarara zuwa kasashen waje da nufin rungumar wannan kaskantacciyar sana'a duk da jan hankalin da hukumomi da kungiyoyi ke yi.
Gwamnatin Jamhuriyar Nijer da Kungiyar Tarayyar Turai sun saka hannu akan wata yarjejeniya wace a karkashinta kungiyar EU ta amince ta ba kasar ta Nijer tallafin biliyan kusan 10 na kudaden cfa wadanda za a yi amfani da su don bunkasa sha’anin ilimi.
Fitaccen dan siyasa a Jamhuriyar Nijar Doudou Rahama na hannun daman tsohon shugaban kasa Mahaman Ousman da magoya bayansa ,sun bada sanarwar canza sheka daga jam’iyar RDR Canji zuwa PNDS Tarayya ta shugaba Mohamed Bazoum.
Domin Kari