Batun sammacin da hukumar yaki da rashawa ta jihar Kano ta ce ta aikawa tsohon gwamnan jihar Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana a gabanta don bada bahasi game da faifan bidiyon da ana ci gaba daukar hankalin kungiyoyi da ‘yan siyasa da kuma masu sharhi kan al’amuran yau da kullum a jihar ta Kano.
A wani mataki na dakile dabi’ar shaye-shaye da kallace-kallacen hotuna da fina-finan batsa a kafofin sadarwa na intanat na zamani tsakanin yara da matasa, wasu kamfanoni da cibiyoyi masu zaman kansu a jihar Kano suka shirya taron lacca domin fadakarwa.
‘Kasa da sa’o’I 24, tsohon gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya mayar da martani dangane da sammacin da hukumar yaki da rashawa da kula da korafin jama’a ta jihar ta ce ta aika masa ya bayyana a gabanta domin bada bahasi kan bidiyon da ake zargi ya nuna yana karbar cin hancin daloli
Kasa da makonni uku Gwamnatin jihar Kano ta ce ta kwato filayen da darajar kudin su ta kai fiye da Naira Triliyon guda daga hannun mutanen da aka mallakawa ta haramtacciyar hanya.
Rashin samun daidaito game da wanda zai jagoranci majalisar jihar ta Jigawa karo na takwas, shi ne ya haifar da tsaiko wajen rantsar da sabbin ‘yan majalisar ranar Talata.
A jihar Kano Najeriya, Hon Jibrin Isma’il Falgore ne ya zama shugaban majalisar dokokin jihar bisa amincewar daukacin ‘yan majalisar su 40. A wani kwarya-kwaryar biki na kaddamar da majalisar ta 10, sabon shugaban ya yi alkawarin tafiya tare da dukkanin ‘yan majalisar domin ciyar da jihar gaba.
Makiyaya da manoma a jihar Jigawa, Najeriya, sun fara tsokaci dangane da yarjejeniyar da hukumomin jihar da na Jihar Zinder a Jamhuriyar Nijar suka sanya wa hannu domin wanzar da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyayan da ke zirga-zirga a sassan jihohin biyu da ke makwaftaka da juna.
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta shirya taron sanin makamar aiki a wani bangare na shirye-shiryen kaddamar da sabuwar Majalisar ta goma da za a gudanar ranar Talata makon gobe.
Sabon gwamnan jihar Jigawa Alhaji Umar Namadi ya ce batun gudanar da garanbawul ga tsarin aikin gwamnati, shine mataki na farko da zai fara dauka kafin aiwatar da ajanda 12 na gwamnatin sa.
Bayan rantsuwar kama aiki, sabon gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ce zai farfado da manufofi, tsare tsare da ayyukan gwamnatin jagoran Jam’iyyar NNPP Rabiu Musa Kwankwaso.
Yayin da damina ke kankama a sassan Najeriya, Kungiyar Manoman shinkafa, sarrafa ta da kuma kasuwancinta ta Najeriya ta kaddamar da Shirin ta na bada lamunin kayan noma na musamman domin karfafa gwiwar manoma.
Bayan rantsar dashi a 29 ga Mayu, Ahmed Bola Tinubu na zaman shugaban Najeriya na 16, a daidai lokacin da yawan ‘yan kasar ya zarta miliyan 200.
Tun gabanin gudanar da zabukan da suka gabata a Najeriya batagarin matasa ke barazana ga mazauna birnin Kano ta hanyar kwace musu wayoyin, musamman a wasu yankuna na birnin walau da rana ko da daddare.
Domin Kari