Kamfanin makamashi na “Mainstream” a Najeriya, wanda tuni yake gudanar da manyan tashoshin samar da wutar lantarki guda biyu a kasar, ya fara gudanar da wani sabon ginin da kasar China ta samar, kusan shekara guda bayan samun wannan damar in ji kamfanin a jiya.
Gwamnatin Bayelsa ta ce za ta ba da fifiko kan koyo da koyar da harsunan Ijaw, da Faransanci, da kuma Sinanci a makarantun gwamnati a jihar.
Wata ma'adina da ake hakar zinari ta bayan fage ta ruguje a karshen makon da ya gabata a kasar Mali, inda ta kashe mutane sama da 70, kamar yadda wani jami'i ya fada jiya Laraba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike bisa fargabar cewa adadin na iya karuwa.
Iran ta fada jiya Laraba cewa, a shirye take ta taimaka wa Jamhuriyar Nijar da aka yi juyin mulki, don shawo kan takunkumin da kasashen duniya suka kakaba mata, a daidai lokacin da Tehran ke kokarin rage maida da ita saniyar ware da aka yi, ta hanyar karfafa alaka da kasashen Afirka.
Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta ta Najeriya ICPC, Dr. Musa Adamu Aliyu, SAN, ya bukaci daliban kasar da su tashi tsaye domin daukar nauyinsu a matsayin masu kawo sauyi da Najeriya ke matukar bukata wajen dakatar da cin hanci da rashawa musamman a makarantu.
Hukumomi a kasar Zambiya sun fada jiya Talata cewa, sun yi ta kokarin tsotse ruwa da laka daga wata ma’adanan tagulla mallakar kasar China inda wasu masu hakar ma’adinai bakwai suka makale a karkashin kasa.
Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana goyon bayanta ga kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta, kwanaki bayan da Firai Ministan Isra'ila ya dauki matsaya mai karfi na rashin son batun samar da kasashe biyu.
An kama wani mutum ranar Talata, kuma zai fuskanci tuhume-tuhume 76 na kisan kai bayan ya bada shaida a bincike cewa shi ya tayar da mummunar gobara a Afirka ta Kudu a bara a lokacin da yake kokarin kawar da gawar wani da ya shake, ya kashe a harabar gidan bisa umarnin wani dillalin miyagun kwayoyi
Wata motar dakon kaya da ke tsananin gudu ta kutsa cikin wani rafi a kudu maso yammacin Kongo, inda ta kashe fasinjoji 18 da ke cikinta tare da jikkata wasu fiye da goma, in ji 'yan sanda
Kasar Kamaru za ta kasance kasa ta farko da za ta rika bai wa yara sabbin rigakafin zazzabin cizon sauro a kai a kai, yayin da ake ci gaba da rarraba allurar ta rigakafi a nahiyar Afirka.
Dexter Scott King, wanda ya sadaukar da yawancin rayuwarsa kan abin da ya gada daga iyayensa Rev. Martin Luther King Jr. da Coretta Scott King na fafutukar kare hakkin dan adam, ya rasu a ranar Litinin bayan ya yi fama da cutar sankara ta prostate. Ya rasu yana da shekaru 62.
Shugaban kasar Amurka Joe Biden, ya bayar da takardar shedar karramawa ga tsohuwar jami’ar sojin saman Amurka, Sarauniya Irene Olasumbo Cole, ‘yar asalin Najeriya, domin sadaukar da kai da ta yi wajen yi wa kasa hidima a rundunar sojin kasar Amurka.
Hajiya Inna Galadima ta jam'iyyar APC, ta zama zababbiyar shugabar karamar hukumar Jere ta jihar Borno, ta kasance Shugabar Karamar Hukuma mace ta farko a jihar.
Shugaban Masar ya ce a ranar Lahadi kasarsa ta tsaya kafada-da-kafada da Somaliya a takaddamar da ke tsakaninta da kasar Habasha na tsakiyar ruwa, wadda ta kulla yarjejeniya da Somaliland domin samun damar shiga teku da kuma kafa sansanin sojojin ruwa.
Gwamnatin jihar Legas a Najeriya ta rufe kasuwar Oke-Afa, Isolo, da Katangua, Abule Egba, bisa karya ka’idojin zubar da shara, da suka hada da rashin tsaftar muhalli a kasuwannin, wadanda ke haifar da munanan laifuka na muhalli.
A wannan watan ne aka cika shekara goma da tsare mai fafutukar kare hakkin ‘dan Adam ta Uighur Ilham Tohti. Tohti wanda ya kasancewa har yanzu a tsare don kawai ya na neman hakkin 'yan Uighurs da sauran tsirarun kungiyoyi dake People’s Republic of China, ko PRC.
Giannis Antetokounmpo shahararran ‘dan wasan kwallon kwando ya lashe lambar yabo ta NBA MVP guda biyu da gasar NBA guda daya. An zabe shi zuwa gasar shahararrun ‘yan wasa kwando karon farko, sau biyar kuma ya buga wasanni bakwai a cikin wasan na fitattun 'yan wasa.
Domin Kari