Sojojin Isra'ila sun kutsawa cikin Jabalia da ke arewacin Gaza a ranar Talata, inda suka kai farmaki kan wani asibiti da lalata wuraren zama da tankokin yaki da bama-bamai ta sama, kamar yadda mazauna yankin suka ce, yayin da jiragen na Isra'ila suka kashe akalla mutum 5 a Rafah da ke kudancin kasar