Wasu ‘yan bindiga da suka yi garkuwa da mutane 105 a yankin Arewa maso yammacin Najeriya a makon da ya gabata, ba kudin fansa su ke so ba, tattaunawa su ke so da gwamnatin jihar Zamfara, kamar yadda wasu iyalai biyar suka shaida bayan da ‘yan bindigar suka tuntube su a ranar Litinin.