Wata mata mai ‘ya’ya biyu ta mutu sanan mutane 21, ciki har da akalla yara takwas, sun raunata a yayin wani harin bindiga da ya auku a wani tashar jirgin kasa mai tarihi da ke birnin na Kansas a Jihar Missouri.
A jiya laraba Amurka ta dorawa wasu mutane 3 da kamfanoni 4 takunkumi a sassan kasashen Iran, da hadaddiyar daular larabawa da Turkiyya, bisa dalilin zargin su da taimakawa wajen fitar da kayayyaki, da sayen fasahohi daga kamfanonin Amurka zuwa kasar Iran da babban bankin kasar.
An sake kama wani mutum da ake nema ruwa a jallo a jihar Massachusetts domin fuskantar tuhumar kisan kai, mako guda bayan ya tsere da dubara daga hannun ‘yan sanda, in ji ‘yan sandan Kenya a ranar Laraba.
Ma’aikatan kashe gobara sun ce mutane shida sun jikkata, kuma mutum daya daga cikinsu na cikin mawuyacin hali sakamakon harbin da aka yi a tashar jirgin karkashin kasa a birnin New York da yammacin jiya Litinin.
An harbe wani yaro dan shekara biyar kuma yana cikin mawuyacin hali a asibiti," a cewar shugaban 'yan sandan birnin Houstan, yayin da wani mutum ke jinyar harbin bindiga a kafa.
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya yi watsi da bukatar kungiyar Hamas na tsagaita wuta tare da ba da umarni ga sojojin kasar da su shirya kutsawa birnin Rafah da ke kudancin Gaza, inda Falasdinawa sama da miliyan daya suka nemi mafaka.
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya isa Saudiyya a yau Litinin a ziyararsa ta biyar a yankin tun bayan barkewar yaki a yankin Gaza, yana fatan ci gaba da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma shiri bayan yakin da dakile tashe-tashen hankula a yankin.
Hukumar wasan kwallon kafa ta duniya ta FIFA, ta sanar ranar Lahadi cewa za a buga wasan karshe na cin kofin duniya na shekarar 2026 a filin wasan Metlife da ke birnin New Jersey.
Amurka ta sake nanata kudurinta na tsayawa tsayin daka a fannin tattalin arziki da kasuwanci a kasashen Afirka.
Wani mutum da ake zargi da fille kan mahaifinsa a birnin Philadelphia, ya wallafa wani bidiyon mai ban tsoro a shafukan sada zumunta wanda ya nuna shi yana rike da kan da ya yanke yana kuma zagin gwamnati, kamar yadda hukumomi suka fada jiya Laraba.
An cafke wani mutum da ake nema kan laifin kashe budurwarsa tare da barin gawarta a wani wurin ajiye motoci a filin jirgin sama na Boston kafin ya tashi zuwa Kenya, kamar yadda ‘yan sandan Kenya suka bayyana a jiya Talata.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.