A ranar Laraba, wasu tankokin yaki guda biyu sun kai hari a matsugunin Majalisar Dinkin Duniya a Khan Yunis inda dubban Falasdinawa da suka rasa matsugunansu suka fake.
Sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken ya hallarci wani taro da bankin raya Afurka ya shirya a birni Legas na samar da abinci da kuma tallafa wa manoman nahiyar.
Dexter Scott King, wanda ya sadaukar da yawancin rayuwarsa kan abin da ya gada daga iyayensa Rev. Martin Luther King Jr. da Coretta Scott King na fafutukar kare hakkin dan adam, ya rasu a ranar Litinin bayan ya yi fama da cutar sankara ta prostate. Ya rasu yana da shekaru 62.
A yayin ziyarar, sakataren zai yi tsokaci kan yadda Amurka ta kara inganta hadin gwiwar Amurka da Afirka tun bayan taron Shugabannin Amurka da Afirka, da suka hada da yanayi, abinci, da kiwon lafiya.
An kebe kowace ranar Litinin na uku (3) a watan Jana'iru a matsayin ranar hutu don tunawa da Dakta Martin Luther King Junior wanda ya jagoranci jerin zanga-zangar lumana tsakanin shekararun 1950 zuwa shekarun 1960.
Sojojin Amurka da na Birtaniyya sun yi ruwan bama-bamai kan 'yan Houthis da ke samun goyon bayan Iran a Yemen a ranar Alhamis, a wani gagarumin harin ramuwar gayya ta hanyar amfani da makamai masu linzami da jiragen yaki na Tomahawk da jirgin ruwan yaki da na karkashin ruwa, in ji jami'an Amurka.
Mahaifiyar Melanie Trump, matar tsohon Shugaban kasar Amurka Donald. Trump, Amalija Knavs, ta rasu, kamar yadda Trump ya tabbatar a wata sanarwa da aka wallafa a X, wanda a da ake kira Twitter. Amalija ta rasu tana da shekaru 78.
A jiya Lahadi manyan shugabannin Majalisar Dokokin Amurka suka amince da kasafin kudin da gwamnatin tarayya zata kashe a shekarar 2024 na dala triliyan 1 da digo 6.
Wani matashi dan shekara 17 ya bude wuta a wata karamar makarantar sakandare ta Iowa a Amurka, a rana ta farkon komawa makaranta bayan hutun hunturu, inda ya kashe wata yarinya ‘yar aji shida tare da raunata wasu biyar a ranar Alhamis yayin da daliban suka yi shinge a ofisoshi a firgice.
A jiya Talata tsohon Shugaban Amurka Donald Trump ya daukaka kara kan hukuncin da sakatariyar harkokin wajen jihar Maine ta jam’iyyar Democrat ta yanke, na haramta masa takara.
"An tabbatar da cewa an kashe Maalim Ayman ne a wani farmakin hadin gwiwa da sojojin kasar Somaliya tare da taimakon sojojin Amurka suka yi a ranar 17 ga watan Disamba," in ji Daud Aweis a shafinsa na X da yammacin ranar Alhamis.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.