Shugaban Amurka Donald Trump a jiya Asabar ya bada amincewar sa ga ci gaba da tsarinn nan da ya zo karshe, na bada tallafin ga miliyoyin Amurkawa da suka rasa ayyukan su a lokacin barkewar annobar coronavirus kana ya dakatar harajin albashi.
Kasashen Rasha da China da kuma Iran suna nan suna shirya katsalanda a zaben shugaban kasar Amurka da zummar Amurkawa su zabi dan takarar da suke so ya shiga fadar White House, a cewar wani muhimmin kashedi da babban jami’in hukumar yaki da masu liken asiri a Washington.
Kasashen duniya na ci gaba da fadi tashin neman makarin cutar COVID-19 a daidai lokacin da kwararru a fannin kiwon lafiya ke nuna shakku kan yiwuwar samun rigakafin cutar a nan kusa, muddin idan ba a bin matakan da suka dace.
Matsananciyar guguwar nan da aka yi wa lakabi da “ISAIAS” tana kara ketawa a tsakiyar jihar New York da New England bayan ta hanzarta ratsawa a yankin tsakiyar Atlantika na Amurka, inda akalla ta kashe mutum hudu.
A jiya Talata Sakataren Harkokin Wajen Amurka Mike Pompeo ya yi alkawarin ba da kariya ga masu rajin demokradiyya a Hong Kong wadanda suka tsere daga garin kuma suka la'anci China bayan da Beijing ta ce, an baiwa 'yan sanda umarnin kama masu fafutukar daga ƙasashen waje.
Jami'an Fadar White House da kuma manyan 'yan jam'iyyar Democrat a majalisar dattawa na shirin sake haduwa, bayan da bangarorin biyu sun bayyana samun ci gaba da kokarin su na yin matsaya kan sabon tallafin gwamnati na cutar coronavirus.
Matsananciyar guguwar nan da aka yi wa lakabi da “ISAIAS” tana cigaba da mamaye gabashin North Carolina.
Rahotannin da ke nuna cewa ayyukan kamfanoni a nan Amurka da ma wasu kasashe sun fara farfadowa daga annobar coronavirus, ya sa kasuwannin hannayen jarin Asia sun zaburo a yau talata.
Masu hasashen yanayi sun yi gargadin cewa iskar Isaias wacce aka yi gargadin cewa za ta tunkari jihohin North da South Carolina za ta Iya zama karamar guguwa.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.