Taron kolin Majalisar Dinkin Duniyar, wanda shine matakin karshe a tsarin diflomasiya, na zuwa ne a daidai lokacin da hukumomin Lebanon suka bayyana cewar hare-haren da Isra’ila ke kaiwa sun hallaka mutane 560 daga cikinsu yara kanana.
Isra’ila da kungiyar Hizbullahi sun cigaba da musayar wuta a yau Talata yayin da adadin mutanen da munanan hare-haren da Isra’ila ke kaiwa suka hallaka ya haura kusa da 560 sannan dubban mutane sun arce daga yankin kudancin Lebanon inda bangarorin biyu ke daf da fadawa cikin kazamin yaki
A yau Talata shugabannin kasashen duniya zasu kaddamar da taron da suke yi a duk shekara a babban zauren MDD a karkashin maudu’an da suka hada da karuwar rabuwar hannu tsakanin al’ummar duniya da manyan yake-yaken dake gudana a Gaza da Ukraine, Sudan da kuma barazar yakin yankin Gabas ta Tsakiya
Daga cikin wadanda aka kashe a hare-haren har da yara 35 da mata 58, a cewar jami'an Lafiyar Lebanon.
A yau Litinin Isra’ila ta kaiwa wuraren Hizbullahi fiye da 100 hari ta sama, al’amarin da hukumomin lafiyar Lebanon suka ce ya hallaka akalla mutane 182, inda ta kasance rana mafi muni a kasar a rikicin da kungiyar dake samun goyon bayan kasar Iran ta shafe kusan shekara guda tana yi.
Kungiyar Hezbullah ta harba jerin makaman roka zuwa yankin arewacin Isra’ila a yau Alhamis, inda ta ci gaba da musayar wuta da dakarun Isra’ila a dai dai lokacin da fargabar kazancewar yaki ke karuwa.
A yau Laraba, a sanarwar da ta wallafa a shafinta na Telegram, kungiyar Hezbollah ta sha alwashin ci gaba da gwagwarmayar tallafawa al’ummar Gaza sannan ta yi alkawarin daukar fansa a kan harin na jiya Talata.
Asibitin Awda, inda aka kai gawawwakin, ya tabbatar da adadin wadanda suka mutun sannan yace an raunata mutane 13. Bayanan asibitin su nuna cewa wadanda suka mutun sun hada da wata uwa da jaririnta da kuma ‘yan uwanta 5.
Wasu fitattun malaman addinin Islama daga Najeriya sun yi kira ga 'yan Afrika mazauna Turai da suka fito kwansu da kwarkwatarsu domin sauraran wa’azi daga bakin maluman a taron da aka saba gudanarwa shekara-shekara a Turai a kan muhimmancin zamantakewa mai kyau.
A kudu maso yammacin Poland, ruwa ya ci mutum daya an kuma sauya wa dubban mutane matsugunni a tsallaken iyaka a Jamhuriyar Czech, yayin da ruwan sama kamar da bakin kwarya ke ci gaba da sauka a tsakiyar nahiyar Turai a yau Lahadi, lamarin da ya haddasa ambaliyar ruwa a wurare da yawa.
Domin Kari
No media source currently available