An sassauta dokar ne da nufin bai wa jama’a damar gudanar da harkokinsu cikin yanayin walwala a tsawon watan nan na Ramadana.
A Jamhuriyar Nijar wasu ‘yan siyasa da jami’an fafutuka sun fara kiraye-kirayen ganin an dakatar da abin da suke kira facaka da kudaden jama’a.
A Jamhuriyar Nijar kungiyoyi masu zaman kansu da shugabanin addinai sun fara jan hankula don ganar da jama’a rashin dacewar bara a matsayin sana’a.
A yayin da a ranar biyu ga watan Afrilu ya cika shekara daya da dare karagar mulki, shugaban kasar Nijer ya bayyana samun nasarori a fannin tsaro a yankunan da ke fama da aiyukan ta’addanci.
Aika aikar ‘yan bindiga akan hanyar Burkina Faso zuwa jamhuriyar Nijer ta fara jefa matafiya cikin halin zullumi ganin yadda wannan al’amari ke kara tsananta a tsakanin wadannan kasashe 2 makwabtan juna.
To amma masu sharhi akan sha’anin tsaro sun gargadi hukumomin akan bukatar matsa kaimi wajen tantance wadanda suka cancanci shiga aikin soja.
A Jamhuriyar Nijar ‘yan kasuwa sun yi barazanar rufe kasuwanni da shagunan kan titi a ranar alhamis mai zuwa.
Gwamnatin jamhuriyar Nijer ta kwashe daruruwan ‘yan kasar da suka tare a kasar Senegal da sunan bara galibinsu mata da yara kanana wadanda suka sauka birnin Yamai a karshen mako kafin daga bisani a mayar da su garuruwansu na asali.
Hukumomin shari’a a jamhuriyar Nijer sun bada sanarwar sallamar akasarin mutanen da suka kama a yayin zanga zangar watsi da sakamakon zaben da aka gudanar a kasar a farkon shekarar 2021 a yayin da a daya bangare ake ci gaba da daukan matakan inganta yanayin rayuwar fursinoni a gidajen yari.
Kungiyar Amnesty International ta bayyana damuwa game da halin kuncin da fursunoni ke ciki a gidan yarin Koutoukale na jihar Tilabery a Jamhuriyar Nijar,
Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta bayyana damuwa a game da abinda ta kira tsadar kujerar hajji sakamakon yadda ejoji ke son cin kazamar riba a cewarta, zargin da tuni suka yi watsi da shi.
A jiya alhamis a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar Ministocin albarkatun ruwa daga kasashen yankin tafkin Chadi sun tantauna da kwararru akan hanyoyin farfado da harakokin yau da kullum a yankin mai fama da matsalolin tsaro.
A Jamhuriyar Nijar Hukumar kula da ayyukan dakon kaya daga tashoshin jiragen ruwa zuwa sassan kasar ta shirya wani taron horo ga masu dakon kaya da ‘yan kasuwar dake shigo da kaya daga waje ta yadda zasu lakanci dubarun da zasu basu damar cin moriyar wannan fanni fiye da yadda abin yake a yanzu.
‘Yan bindiga sun afka wa wata motar jigila mai dauke da fasinjoji sama da 40 akan hanyarsu ta zuwa birnin Yamai bayan da suka fito daga birnin Ouagadougou na kasar Burkina Faso, cikinsu har da ‘yan sanda uku.
Kungiyar REJEA mai fafitikar samar da ruwan sha ta shirya wani taron hadin guiwa da gidauniyar Noor ta uwargidan shugaban kasa Hajiya Hadiza Bazoum da nufin tayar da hukumomi da masu hannu da shuni daga barci akan maganar samar da wadatar ruwan sha mai tsafta .
A yayin da hukumomin Nijer suka ayyana shirin gabatar wa majalisar dokokin kasa bukatar samun hadin kanta wajen girke dakarun rundunar Barkhane a kasar bayan ficewar rundunar daga Mali, kwamandan rundunar ta kasar Faransa ya ce kai tsaye zasu koma gida a maimakon zuwa wata kasar waje.
Domin Kari