A jamhuriyar Nijar shugabanin kungiyar ‘yan tawayen UFPR sun ba da sanarwar ajiye makamai bayan da suka gana da shugaba Mohamed Bazoum a fadarsa a karshen mako.
Majalisar dokokin jamhuriyar Nijar ta amince da dokar tsawaita shekarun ritayar ma’aikatan gwamnati, matakin da kungiyoyin kwadago suka yi na’am da shi yayin da su kuma matasa ke ganin abin tamkar wani shingen da zai hana su samun aiki da wuri.
A jamhuriyar Nijar, a karo na biyu a kasa da mako daya hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kama wasu mutane dauke da tan kusan daya na tabar wiwi a lokacin da suka yi kokarin tsallaka kogin Kwara da ke yankin iyakar Nijar da jamhuriyar Benin da ma Najeriya.
A jamhuriyar Nijar gamayyar kungiyoyin fafutuka ta M-62 ta shigar da bukata a hukumar yaki da cin hanci, ta gurfanar da tsohon shugaban kasar Mahamadou Issouhou a gabanta.
A jamhuriyar Nijar wasu jami’an tsaron kasar sun mutu bayan da motarsu ta taka nakiya lokacin da suke aikin sintiri a jihar Tilabery mai fama da aika-aikar ‘yan ta’addan da ke da sansannoni a kasashen Mali da Burkina Faso.
Dalibai kimanin 47 da suka makale a Sudan sun sauka birnin Yamai a cikin daren laraba bayan da suka shafe kwanaki uku a tsakanin biranen Khartum da N’Djamena, suka ratsa ta Angola kafin su isa gida cikin wani jirgin da gwamnatin Nijer da tura kasar Tchad.
A cikin shirin na wannan makon, rashin ayyukan yi ko jarin tsira kasuwanci wata matsala ce da ke daga hankulan masu bukata ta musamman a Ghana.
Hukumomin jamhuriyar Nijar sun kama shugaban kungiyar kare muradan jama’ar jihar Tilabery da shugaban wata jam’iyyar hamayya saboda zarginsu da furta kalaman da ke barazana ga zaman lafiya, sai dai wasu ‘yan fafutika na daukar matakin a matsayin bita da kullin siyasa.
Masu Sharhi sun bayyana damuwa dangane da makomar bakin da suka makale a Sudan sakamakon yadda aka fara zargin wasu bakin da zama sojan hayar da ke kama wa bangaren ‘yan tawaye.
Wani binciken kasa da kasa ya bankado bayanan dake nuna alamun hannun tsohon shugaban kasa Issouhou Mahamadou a badakalar da karkashinta ake zargin mahukuntan Nijer sun hada kai da kamfanin Areva don sayar da tonne 2500 na karfen uranium ta bayan fage a shekarar 2011.
A cikin shirin na wannan makon; a makon da ya gabata shirin ya sauka a jihar Agadez dake yankin arewacin jamhuriyar Nijar inda a kashi na farko muka tattauna da shugaban kungiyar nakasassu na jihar Abdou Moutsallabi.
Gwamnatin Nijar ta ce ta samu nasarar kwashe jami’an diflomasiyyarta daga Sudan zuwa Djibouti a wani kokarin hadin gwiwa da kasar Faransa, sai dai wasu ‘yan kare hakkokin bil’adama na ganin ba a yi wa dalibai da sauran ‘yan Nijar mazauna Sudan adalci ba saboda yadda aka bar su a Khartoum.
A jamhuriyar Nijar, direbobin motocin dakon itacen girke-girke sun bayyana damuwa dangane da abinda ka iya zama makomar wannan fanni da ke matsayin hanyar makamashin miliyoyin ‘yan kasar.
Hukumar sadarwar jamhuriyar Nijar, ta kudiri aniyar samar da karin kudaden tallafi ga kafafe yada labarai masu zaman kansu kamar yadda abin yake a wasu kasashen yammacin Afrika ta yadda za su kara inganta ayyukan watsa labarai da tsara shirye-shiryen ci gaban kasa.
Kungiyar hadin kan kabilun Nijar wato NSC a takaice ta shirya bikin rarraba tufafin sallah da kayan abinci domin yara marayu da nufin ba su damar samun walwala kamar sauran yaran da iyayensu ke raye.
Ma'aikatar harkokin wajen Nijar ta tabbatar da labarin kama wasu ' yan kasar a Saudiya dake dauke da miyagun kwayoyi. Sai dai kawo yanzu ba a yanke musu hukunci ba kuma ba a san makomar su ba a cewar hukumomi.
Shugabanin kungiyoyin manoman albasa da masu fitar da ita kasashen ketare sun koka a game da babbar asarar da matsalolin tsaro ke haddasa wa wannan fanni inda ‘yan ta’addan Burkina Faso ke kona motoci dauke da lodin albasa akan hanyarsu ta zuwa Cote d'Ivoire da Ghana
‘Yan adawa a Majalisar dokokin Jamhuriyar Nijer sun bayyana damuwa dangane da yadda bangaren rinjaye ke haddasa cikas ga tsarin sulhun dake tsakanin bangarorin siyasar kasar.
Hukumomin Jamhuriyar Nijar da hadin guiwar kamfanin SONIMA sun kaddamar da ayyukan rajistar kananan bindigogin da ke hannun jama’a da nufin tantance fararen hular da suka mallaki makamai don takaita hadarin da ke tattare da rike bindiga ba akan ka’ida ba.
Domin Kari