Wani rahoton da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar a karshen makon jiya ya ayyana cewa kungiyar IS ta yi nasarar ninka hare-haren da take kai a kasar Mali sau biyu a tsawon shekara cikin shekara guda, abin da ke fayyace girman mamayar da kasar ta Mali ke fuskanta daga kungiyoyin ta’addanci.
Hukumomin Nijar sun umarci jakadan Faransa Sylvain Itte da ya fice daga kasar a cikin sa'o'i 48 daga ranar Juma’a 25 ga watan Agusta, sai dai ma’aikatar harakokin wajen Faransa a na ta bangare ta yi watsi da matakin.
Gwamnatin rikon kwaryar Jamhuriyar Nijar ta amince wa dakarun kasashen Mali da Burkina Faso su shiga kasar don bin sawun ‘yan ta’adda a duk lokacin da bukatar hakan ta taso a ci gaba da karfafa matakan yaki da kungiyoyin jihadin da suka addabi yankin Sahel.
A karo na biyu a cikin kasa da mako biyu, wata tawagar Malaman addinin Islama daga Najeriya ta kai ziyaraa jamhuriyar Nijar a yammacinranar Laraba, inda suka gana da Shugaban sojojin da suka yi juyin mulki Janar Abdourahaman Tchiani da Firai Minista Ali Mahaman Lamine Zeine.
Babban alkali mai shigar da kara a kotun daukaka kara ta birnin Yamai ya yi kashedi ga wasu wadanda ya ce suna yada labarai da kalaman da ke barazanar ta da fitina a wani lokacin da ake matukar bukatar ganin ‘yan Nijar sun kasance tsintsiya madaurinki daya.
Wani harin ta’addancin da aka kai a kauyukan jihar Tilabery da ke Nijar ya yi sanadin rasuwar jami’an tsaro da dama a lokacin da suke kokarin kwato tarin shanu da maharan suka sace a karkarar Anzourou.
Shugaban majalissar sojojin da suka yi juyin mulki a jamhuriyar Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani ya bayyana fatan gudanar da al’amuran mulkin rikon kwaryar na tsawon wa’adin da bai kamata ya wuce shekaru uku ba.
Wannan tawagar ta je Jamhuriyar Nijar ne karo na biyu da nufin tantaunawa da sojojin da suka yi juyin mulki a kasar a ranar 26 ga watan Yulin 2023.
Daruruwan daliban Jamhuriyar Nijar da ke fatan shiga jami’oin Faransa sun fada halin zullumi sakamakon rashin samun takardar biza bayan da gwamnatin Faransar ta rufe ofishin jakadancinta a birnin Yamai sanadiyyar yanayin siyasar da aka shiga a kasar.
Wasu sabbin hare-haren da aka kai a jihar Tilabery ta Jamhuriyar Nijar sa’o'i bayan kisan wasu dakarun tsaro 17 a yankin mai fama da ayyukan ‘yan ta’adda, sun yi sanadin mutuwar gwamman fararen hula, abin da manazarta ke bayyanawa a matsayin girman matsalar tsaron da ta addabi kasashen Sahel.
Sai dai makusantan tsohon shugaban sun musanta wannan zargi, suna masu cewa har da dansa aka tsare a juyin mulkin da aka yi.
Masu fashin kan sha'anin tsaro sun ce matsalar hare-haren na da alaka da tsamin dangantaka da aka samu tsakanin Nijar da Faransa bayan juyin mulkin da aka yi.
Wannan sabuwar dambarwa ta kunno kai ne kwana guda bayan da wata tawagar manyan malaman addinin Islama daga Najeriya ta kai ziyarar shiga tsakani a rikicin siyasar kasar.
Wata tawagar malaman addinin Islama ta ziyara a birnin Yamai a ranar Assabar inda suka gana da shugabannin mulkin sojin jamhuriyar Nijar da suka hada da Janar Abdourahamane Tchiani da Firai Minista Ali Mahaman Lamine Zeine.
Wasu 'yan Nijar na ganin Faransa ba ta tabuka wani abin a-zo-a-gani a yakin da take yi da ayyukan ta'addanci a kasar da ma yankin Sahel baki daya.
Sabuwar gwamnatin ta rikon kwarya wacce Firai Minista, kuma Ministan kudin kasa Ali Mahaman Lamine Zeine zai jagoranta na da mambobin 21
Sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar sun zargi kasar Faransa ta kai hari kan wasu askarawan kasar da sanyin safiyar yau Laraba 9 ga watan Agusta a wani kauyen Jihar Tilabery, abin da ya haddasa asarar rayuka, koda yake kawo yanzu ba a tantance adadinsu ba.
Sojojin da suka yi juyin mulki a jamhuriyar Nijer sun nada Ali Mahaman Lamine Zeine a matsayin Firai Ministan Gwamnatin rikon kwaryar da suke shirin kafawa a dai dai lokacin da karamar sakatariyar Amurka mai kula da harakokin siyasa Victoria Nuland ta kai ziyara a Nijar.
Domin Kari