Wata hira ta musamman da wani mai sharhi a kan al'amuran yau da kullum a Nijar game da rashin Zartas da kudurin CEDEAO.
A yayinda wa’adin da ECOWAS ta bayar don mayar da shugaban Nijar Mohamed Bazoum kan mukaminsa ya shude a jiya Lahadi, sojojin da suka yi juyin mulki sun kara tsaurara matakai da nufin tunkarar barazanar amfani da karfin sojan da kungiyar ECOWAS ta ayyana don korarsu daga fadar ta shugabancin Nijar.
Gwamnatin mulkin sojan ta Nijar, ta sallami wasu jakadun kasar da suka hada da na Amurka, Faransa, Najeriya da Togo.
Jam'iyyar PNDS Tarayya ce ta sanar da wannan matakin da sojojin suka dauka yayin da a daya gefen kuma hukumomin sojin ba su ce uffan ba kan lamarin.
Jagoran sojojin da suka yi juyin mulki ya yi wannan ikirarin ne a wani lokacin da ake jiran zuwan tawagar ECOWAS/CEDEAO karkashin jagorancin Janar Abdulsalami Abubakar domin samo bakin zaren wannan rikici cikin ruwan sanyi.
Manazarta sha’anin tsaro na ci gaba da bayyana matsayinsu dangane da barazanar amfani da karfi da kungiyar CEDEAO ta yi wa sojojin Nijer akan bukatar su mayar da hambararen shugaba Mohamed Bazoum kafin cikar wa’adin mako daya.
Haka kuma majalisar sojojin ta sanar da bude iyakokin kasar ta Nijar da wasu kasashen da ba su da alaka da ECOWAS.
A yayin da gwamnatin Faransa ta ayyana shirin kwashe ‘yan kasarta daga Nijar, kasashen Mali da Burkina Faso sun jaddada goyon baya ga sojojin da suka yi juyin mulki a kasar.
A jamhuriyar Nijar kungiyoyin rajin kare hakkin bil adama sun bukaci bangarorin da ke takaddama a rikicin siyasar da ya sarke a kasar da su rungumi hanyar sulhuntawa da juna.
Shugaban kasar Chadi ya isa birnin Yamai a yammacin ranar Lahadi jim kadan bayan kammala taron kungiyar kasashen ECOWAS.
Shugabanin kasashen kungiyar ECOWAS za su gudanar da taro a Abuja don tantauna inda zasu bullo wa sojojin da suka yi juyin mulki a jamhuriyar.
Jam’yar PNDS Tarayya madugar kawancen jam’iyun hambarariyar gwamnatin Nijar ta musanta zargin hannun tsohon Shugaban kasa Issouhou Mahamadou, a juyin mulkin da soja suka yi wa Mohamed Bazoum a ranar Larabar ta gabata.
Sojojin da suka kifar da shugaba Mohamed Bazoum a ranar Larabar da ta gabata a Jamhuriyar Nijar sun zabi kwamandan rundunar tsaron fadar Shugaban kasa General Abdourahamane Tchiani a matsayin shugaban majalissar CNSP domin ya jagoranci al’amuran kasar.
Wasu masu zanga-zangar goyon bayan sojojin da suka yi juyin mulki a kasar sun yi kaca-kaca da ofishin jam’iyar PNDS mai mulki a yau Alhamis tare da kwasar ganima da farfarsa gilasai da kona gomman motoci.
Bangarorin siyasa a Jamhuriyar Nijar sun fara maida martani bayan da wasu sojoji suka ba da sanarwar kifar da shugaba Mohamed Bazoum daga karagar mulki a ranar Laraba 26 ga watan Yuli, yayin da jam’iyar PNDS mai mulki ke cewa za ta yi gwagwarmaya don mayar da hambararen shugaban akan kujerarsa.
Ta tabbata sojoji sun yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijer a jiya laraba.
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta kafa wannan dokar ne ta hana fitar da hatsi da shinkafa daga kasar a matsayin wani mataki na kare karancin abinci a kasuwannin kasar.
Ministan cikin gidan Jamhuriyar Nijar ya ziyarci wasu gundumomin jihar Tilabery da nufin kwantar da hankulan mutanen da suka tsere daga matsugunansu bayan da a farkon watan nan na Yuli ‘yan ta’adda suka umurce su da su fice daga garuruwan ko kuma su kuka da kansu da abin da zai biyo baya.
Gwamnatin jamhuriyar Nijer ta kaddamar da ayyukan gina daruruwan rijiyoyin burtsatse masu aiki da hasken rana a yankunan karkara musamman wadanda ke fama da matsalar ruwan sha da nufin samar wa al’umma wadataccen ruwa mai tsafta.
Domin Kari