Mafi akasarin 'yan sandan Najeriya na wajen gadin ministoci, gwamnoni, sanatoci da manyan ma'aikatan gwamnati, in ji Aleiro.
Wasu hare-hare da kungiyar ta kai a shekarar 2016, sun gurguntar da adadin man da kasar ke hakowa a rana.
“Za mu ci gaba da tattaunawa da masu ruwa da tsaki don tabbatar da tsaro a makarantu.” Shugaban na NANS ya ce.
Dan wasan Belgium Thorgan Hazard ne ya zira kwallon kafin a je hutun rabin lokaci, abin da ya kwaci kasar a karawar da suka yi a zagayen ‘yan 16.
Matawalle ya dare karagar mulkin jihar karkashin tutar jam’iyyar PDP, bayan da kotun koli ta soke nasarar da APC ta samu a zaben 2019.
“Ma’aikatar lafiya ta yi matukar mamaki, da muka ji labarin shugabar ta dauki wannan mataki. Mun kuma kwashe lokaci muna bincike kafin mu aika mata da wannan wasikar tuhuma.”
Rundunar sojojin Najeriya ta yi ikirarin kashe ‘yan bindiga da dama a yankin Talata Mafara da ke jihar Zamfara.
Fadar shugaban kasar ba ta bayyana dalilin dage tafiyar ba, amma ta ce nan gaba za a bayyana wata rana daban.
Idan ya nuna halayya mai kyau yayin zaman gidan yarin, akwai yiwuwar a saki Chauvin nan da shekara 15 - amma zai ci gaba da rayuwa karkashin sa idon hukuma.
Shugaban zai dawo cikin mako na biyu a watan Yuli kamar yadda wata sanarwa da fadarsa ta fitar a ranar Alhamis.
A cewar Akinwumi, gabanin barkewar annobar, akwai kasashe 6 a nahiyar da tattalin arzikinsu ya hau turbar zama tattalin arzikin da ke bunkasa a duniya.
A lokuta da dama, akan zargin Fulani ne da kai hare-hare a jihar da ma sauran jihohin da ke arewa maso yammacin Najeriya, amma Gotomo ya ce su ba sa goyon bayan wannan aika-aika.
Sakamakon wannan wasa na nufin dukkan kasashen biyu, sun shiga zagayen ‘yan 16 da iyawar kowa za ta fisshe shi.
Da yawa daga cikin ‘yan Najeriyar da ke tafka muhara a kafafen sada zumunta, sun kwatanta wannan al’amari a matsayin abin kunya ga kasar yayin da shugabannin majalisar ke cewa ba laifinsu ba ne.
Kazalika, an nada Janar Abayomi Gabriel Olonisakin mai ritaya wanda shi ne tsohon hafsan hafsoshin Najeriya a matsayin jakadan kasar a Kamaru.
Matakin da kotun ta dauka na zuwa ne, sa'o'i bayan da shugaban Najeriya ya amince da samar da wata tawaga da za ta yi zaman sasantawa da Twitter.
A ‘yan kwanakin nan an yi ta kai hare-hare a kewayen jihar, wadanda suka yi sanadin mutuwar mutane da dama.
“Da wannan babban kifi yana cikin korama amma yanzu wannan babban kifi ya shigo cikin teku.” Ganduje ya ce a lokacin da Zango ya kai masa ziyara.
Lawal shi ne tsohon shugaban kwamiti a Majalisar wakilai da ke sa ido kan harkar kudaden tallafin mai a Najeriya.
Sama da mutum miliyan 39 na amfani da shafin na Twitter a Najeriya, adadin da ya fi na kowacce kasa da ke nahiyar Afirka kamar yadda kididdigar baya-bayan nan ta nuna.
Domin Kari