A lokuta da dama, akan zargin Fulani ne da kai hare-hare a jihar da ma sauran jihohin da ke arewa maso yammacin Najeriya, amma Gotomo ya ce su ba sa goyon bayan wannan aika-aika.
Sakamakon wannan wasa na nufin dukkan kasashen biyu, sun shiga zagayen ‘yan 16 da iyawar kowa za ta fisshe shi.
Da yawa daga cikin ‘yan Najeriyar da ke tafka muhara a kafafen sada zumunta, sun kwatanta wannan al’amari a matsayin abin kunya ga kasar yayin da shugabannin majalisar ke cewa ba laifinsu ba ne.
Kazalika, an nada Janar Abayomi Gabriel Olonisakin mai ritaya wanda shi ne tsohon hafsan hafsoshin Najeriya a matsayin jakadan kasar a Kamaru.
Matakin da kotun ta dauka na zuwa ne, sa'o'i bayan da shugaban Najeriya ya amince da samar da wata tawaga da za ta yi zaman sasantawa da Twitter.
A ‘yan kwanakin nan an yi ta kai hare-hare a kewayen jihar, wadanda suka yi sanadin mutuwar mutane da dama.
“Da wannan babban kifi yana cikin korama amma yanzu wannan babban kifi ya shigo cikin teku.” Ganduje ya ce a lokacin da Zango ya kai masa ziyara.
Lawal shi ne tsohon shugaban kwamiti a Majalisar wakilai da ke sa ido kan harkar kudaden tallafin mai a Najeriya.
Sama da mutum miliyan 39 na amfani da shafin na Twitter a Najeriya, adadin da ya fi na kowacce kasa da ke nahiyar Afirka kamar yadda kididdigar baya-bayan nan ta nuna.
Taron matasan na APC na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriyar ta tsinci kanta a cikin wani yanayi na kiraye-kirayen da kungiyar IPOB ke yi na a raba kasar.
Tsintsiya ita ce alama ko tambarin jam’iyyar APC wacce ta karbi mulkin Najeriya a shekarar 2015.
Kalaman shugaban na EFCC na zuwa ne a lokacin da aka tambaye shi inda aka kwana dangane da wasikar da EFCC ta taba aikawa Tinubu kan ya bayyana kadarorin da ya mallaka.
"An kubutar da malami daya da dalibai uku a yankin Makuku, sannan sojoji sun kashe dan bindiga daya sun kuma kwato babura tara da wayoyin hannu hudu daga ‘yan bindigar da ke tserewa."
Yanzu Pillars na matsayi na uku da maki 49 yayin da Akwa United ta dare sama da maki 53 a teburin gasar ta Premier a Najeriya.
A ranar Lahadi Zulum ya yi rangadin yankin hanyar ta Mulai zuwa Dalwa don ganewa idonsa yadda za a tsara bude hanyar.
Makonni biyu da suka gabata hukumomin Najeriya suka haramta amfani da shafin wanda suka ce yana barazana ga zaman lafiyar kasar.
“Wanda bai sani ba ya sani, Hassan Mai Daji kanin mahaifiyata ne. Saboda haka, na kira gayya za mu shiga daji.”
Tsohon shugaban babban bankin kasar Abdolnasser Hemmati, wanda ya yi takara da Raisi ya amince da shan kaye.
Eriksen ya yanke jiki ya fadi ne a lokacin da suke karawa da Finland a gasar cin kofin turai ta 2020 da ke wakana a sassan nahiyar a ranar 13 ga watan Yuni.
Naja’atu ta fara fitowa a finan-finan Kannywood tun tana ‘yar matashiya inda daga baya ta zama daya daga cikin fitattun jarumai mata.
Domin Kari