Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Buhari Ya Fasa Tafiya London Duba Lafiyarsa


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari

Fadar shugaban kasar ba ta bayyana dalilin dage tafiyar ba, amma ta ce nan gaba za a bayyana wata rana daban.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya dage ziyarar da zai kai birnin London na Birtaniya don duba lafiyarsa.

Wata sanarwa da kakakinsa Femi Adesina ya fitar a ranar Juma'a ce ta bayyana hakan.

Sai dai fadar shugaban kasar ba ta bayyana dalilin dage tafiyar ba.

"Za a bayyana ranar da zai yi tafiyar a nan gaba." In ji Adesina.

A ranar Alhamis fadar shugaban kasar ta sanar da cewa Buharin zai tafi London a ranar Juma’a don sake ganin likita.

Buhari zai tafi birnin London na kasar Birtaniya a ranar Juma’a, 25 ga watan Yuni 2021, don komawa ya sake bibiyar lafiyarsa.” Wata sanarwa da kakakinsa Femi Adesina ya fitar ta ce.

Karin bayani akan: London, Birtaniya, Shugaba Muhammadu Buhari, Nigeria, da Najeriya.

A baya an tsara akan cewa shugaban zai dawo a mako na biyu cikin watan Yulin da ke tafe a cewar Adesina.

A watan Maris Buhari ya je kasar ta Birtaniya inda ya je duba lafiyarsa, ya kuma kwashe kusan mako biyu a can kafin ya koma gida.

Da tafiyar ta yi wu, da ta kasance ziyara ta biyu cikin kasa da wata uku da shugaban zai kai London don ganin likita.

A shekarun baya, shugaban na Najeriya ya kan je a duba lafiyarsa, illa a bara da bai je ba, saboda annobar COVID-19 da ta karade duniya, ta kuma sa aka rufe hanyoyin tafiye-tafiye.

XS
SM
MD
LG