An jima ana neman Modu ruwa a jallo, saboda irin rawar da yake takawa wajen kitsa ayyukan ta’addanci a cewar sojojin Najeriya.
Brazil ce a saman teburin da maki 24, Argentina a matsayi na biyu da maki 18 sai Uruguay da maki 15 baya ga Ecuador mai maki 13 da Columbia mai maki 13 ita ma.
Sai dai kwamishinan yada labarai a jihar ta Imo Declan Emelumba, ya ce akwai manyan ayyuka guda hudu da ake sa ran shugaba Buhari zai kaddamar a lokacin ziyarar.
Sallamar Mohammed na zuwa ne kasa da wata hudu bayan da aka nada shi a mukamin.
Saka dokar ta biyo bayan rikici da birnin Jos ya fuskanta a ‘yan kwanakin nan wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da asarar dukiyoyi.
Williams ya fara shiga fannin nishadi ne a matsayin dan rawa inda ya fito a wakokin Missy Elliot, Ginuwine, Crystal Waters da kuma Technotronic.
“Mun yi amannar cewa, sana’ar cajin waya, wani fanni ne da yake taimakawa ‘yan fashin daji wajen samun hanyoyin sadarwa.”
A ‘yan kwanakin da suka gabata Jos, babban birnin jihar da kewayensa, ya tsunduma cikin rikici lamarin da ya yi sanadiyyar asarar rayuka da dumbin dukiyoyi.
Dan shekara 80, Pele, shi ne dan wasan kwallon kafa namiji da ya taba lashe kofin duniya sau uku.
Chambas ya nuna fargabarsa kan yadda nahiyar Afirka musamman yankin yammaci yake fadawa kangin juyin mulki.
A ranar 7 ga watan Nuwambar 2010, Alpha Conde ya zama shugaban Guinea na farko da aka zaba bisa tsarin dimokradiyya.
A watan Oktoba shugaba Alpha Conde ya lashe zabe a karo na uku bayan da ya yi wa kundin tsarin mulkin kasar kwaskwarima, abin da ya ba shi damar sake tsayawa takara duk da cewa ya kammala wa’adinsa na biyu.
Kamfanin dillancin labaran AFP ya ruwaito a ranar Lahadi cewa ya samu wani bidiyon shugaba Alpha Conde sanye da wata riga da wando da suka yamutse, yana zaune a wata kujera zagaye da sojoji.
Faransa ce ke saman teburin da maki tara a wasanni biyar da ta buga amma Finland wacce ke matsayi na biyu da maki biyar na da wasanni biyu da za ta buga a nan gaba.
Hukumomin tsaro sun ce ‘yan bindigar da suka kashe Olajide sun sace wasu mutane biyar da suke tare da shi.
Matsalar garkuwa da mutane ta zama ruwan dare a Najeriya musamman a arewa maso yammacin kasar, inda ‘yan bindiga suka mayar da satar mutane don neman kudin fansa tamkar sana'a.
Domin Kari